< Isaiah 40 >

1 Our God says, “Encourage my people! Encourage them!
Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
2 Speak kindly to [the people of] Jerusalem; tell them that their suffering is ended, and that I have forgiven them for the sins that they have committed; I [SYN] have fully punished them for their sins.”
Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
3 I hear someone who is shouting, “Prepare in the desert a way for Yahweh to come [to you]; make a smooth road for our God (OR, Prepare yourselves to receive Yahweh when he comes, like people make a straight road for an important official [MET]).
Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
4 Fill in the valleys; flatten every hill and every mountain. Make the uneven ground smooth, and make the rough places smooth.
Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
5 [If you do that], it will become known that Yahweh is glorious/great, and all people will realize it at the same time. [Those things will surely happen] because it is Yahweh who has said [MTY] it.”
Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
6 Someone said to me, “Shout!” I replied, “What should I shout?” [He replied], “[Shout that] people are like [SIM] grass; their influence fades as quickly as flowers in the field.
Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
7 Grass withers and flowers dry up when Yahweh causes a hot wind from the desert to blow on them. And people are [MET] like that.
Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
8 The grass withers and the flowers dry up, but what our God promises will last forever.”
Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
9 You [people of] Jerusalem, you have good news to tell to people, so, shout it from the top of a high mountain! Shout it loudly, and do not be afraid! Tell the people in the towns of Judah, “Your God is coming here!”
Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
10 Yahweh your God will be coming with power; he will rule powerfully [MTY]. And when he comes, he will bring with him the people whom he has freed [MET] [from being slaves in Babylonia].
Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
11 He will take care of his people like [SIM] a shepherd takes care of his sheep, and carries the young lambs in his arms. He carries them close to his chest and he gently leads the female sheep that are nursing their young lambs.
Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
12 [There is no one like Yahweh]! (Who else has measured the water in the oceans in the palm of his hand?/No one else has measured the water in the oceans in the palm of his hand!) [RHQ] (Who else has measured the sky with his fingers?/No one else has measured the sky with his fingers!) [RHQ] (Who else knows how much the earth weighs?/No one else knows how much the earth weighs!) [RHQ] (Who else has weighed the mountains and hills on scales?/No one else has weighed the mountains and hills on scales!) [RHQ]
Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
13 And (who else can advise Yahweh’s Spirit?/No one else can advise Yahweh’s Spirit!) [RHQ] (Who can teach him or advise/tell him what he should do?/No one can teach him or advise/tell him what he should do!) [RHQ]
Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
14 (Has Yahweh consulted anyone else to get advice?/Yahweh has certainly not consulted anyone else to get advice!) [RHQ] (Does he need someone to tell him what is right to do and how to act justly?/He certainly does not need someone to tell him what is right to do and how to act justly!) [RHQ]
Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
15 [Yahweh considers that] the nations are [as insignificant as] [MET] one drop from a bucket [full of water]. They are [as insignificant as] dust on scales. He is able to weigh islands [as though they weighed no more than] grains of sand.
Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
16 There would be [not] enough wood from all the trees in Lebanon to make a suitable fire for [sacrificing animals to] him, and there are not enough animals in Lebanon to offer as sacrifices to him.
Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
17 The nations of the world are completely insignificant/unimportant to him; he considers that they are worthless and less than nothing [HYP, DOU].
A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
18 So, to whom can you compare God? What image resembles him?
To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
19 Can you compare him to an idol that is made in a mold, and then is covered with [a thin sheet of] gold and decorated with silver chains?
Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
20 A man who is poor [cannot buy silver or gold for his idol]; [so] he selects a piece of wood that will not rot, and he gives it to a craftsman to carve an idol that will not fall down!
Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
21 Have you(pl) not heard this? Do you not understand it? Are you unable to hear what God said long ago— [messages that he gave] before he created the earth?
Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
22 God sits [on his throne] above the earth, and the people [on the earth] below seem to be [as small] as [SIM] grasshoppers. He spreads out the sky like a curtain; it is like [SIM] a tent for him to live in.
Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
23 He causes kings to have no more power, and he causes the rulers to be worth nothing.
Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
24 They start to rule, like small plants start to grow and form roots; but then [he gets rid of them] as though [MET] they withered when he blew on them, like [SIM] chaff that is blown away by the wind.
Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
25 The Holy One asks, “To whom will you compare me? Is anyone equal to me?”
“Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
26 Look up toward the sky: Consider who [RHQ] created all the stars. [Yahweh created them], and at night he causes them to appear; he calls each one by its name. Because he is extremely powerful [DOU], all of the stars are there [LIT] [when he calls out their names].
Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
27 You people of Israel [DOU], why do you complain that Yahweh does not see the [troubles that you are experiencing]? Why do you say that he does not act fairly toward you?
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
28 Have you never heard and have you never understood that Yahweh is the everlasting God; he is the one who created the earth, [even the] most distant places on the earth. He never becomes weak or weary, and no one can find out how much he understands.
Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
29 He strengthens [DOU] those who feel weak and tired.
Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
30 Even youths become faint and weary, and young men will fall when they are exhausted.
Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
31 But those who trust in Yahweh will become strong again; [it will be as though] they will soar/fly high like [SIM] eagles do. They will run [for a long time] and not become weary; they will walk [long distances] and not faint.
amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.

< Isaiah 40 >