< Isaiah 4 >

1 When that happens, [there will be very few unmarried men still alive]. [As a result], seven [unmarried] women will grab one man, and say, “Allow us [all] to marry you [IDM]! We will provide our own food and clothing. All that we want is to no longer be disgraced [because of not being married].”
A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
2 [But] some day, Israel [MTY] will be [very] beautiful and great/glorious. The people of Israel who will still be there will be very proud of the wonderful fruit that grows in their land.
A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
3 All the people who will remain in Jerusalem, who were not killed when Jerusalem was destroyed, whose names are listed among those who live there, will be [called] holy.
Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
4 [That will happen when] Yahweh washes away the guilt of the women of Jerusalem, and when he stops the violence [MET] [on the streets of Jerusalem] by punishing [the people of Jerusalem]. When he does that, it will be like a fire to burn up all the impure things.
Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
5 Then Yahweh will send a cloud of smoke every day and a flaming fire every night to cover Jerusalem and [all] those who gather there; it will be [like] a glorious canopy over the city
Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
6 that will shelter the people from the sun during the daytime and protect them when there are windstorms and rain.
Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.

< Isaiah 4 >