< Isaiah 35 >

1 [Some day, it will be as though] the desert [and other very] dry areas are glad [DOU]; the desert will rejoice and flowers will blossom. Like crocuses/daffodils,
Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
2 the desert will produce flowers abundantly; [it will be as though] everything is rejoicing and singing! The deserts will become as beautiful as [SIM] [the trees in] Lebanon, as fertile [SIM] as the plains of the Sharon and Carmel [areas]. [There] people will see the glory of Yahweh; they will see that he is magnificent.
zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
3 [So], encourage those who are tired and weak.
Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
4 Say to those who are afraid, “Be strong and do not be afraid, because our God is going to come to get revenge [on his enemies]; he will (pay them back/punish them) for what they have done, and he will rescue you.”
ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
5 When he does that, [he will enable] blind people to see and [enable] deaf people to hear.
Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
6 Lame people will leap like deer, and those who have been unable to speak will sing joyfully. Water will gush out [from springs] in the desert; streams will flow in the desert.
Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
7 The very dry ground will become a pool of water, and springs will provide water for the dry land. Grass and reeds and papyrus will grow in places where the jackals/wolves lived previously.
Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
8 And there will be a highway through that land; it will be called ‘the Holy Highway’. People who are not acceptable to God will not walk on that road; it will be only for those who conduct their lives as God wants them to; foolish people will become lost while walking on that road.
Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
9 There will not be any lions there or any other dangerous animals along that road. Only those who have been freed [from being slaves in Babylonia] will walk on it.
Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
10 Those whom Yahweh has freed will return to Jerusalem; they will sing as they enter the city; they will be extremely joyful [MET, PRS] forever. No longer will they be sad or mourn; they will be [completely] joyful [DOU].
kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.

< Isaiah 35 >