< Isaiah 32 >
1 Listen to this! Some day there will be a righteous king, and his officials will help him to rule justly/fairly.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 Each [of them] will be like [MET] a shelter from the wind and a (refuge/place to be protected) from the storm. They will be like [SIM] streams of water in the desert, like the shade under a huge rock in a very hot and dry land.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 When that happens, [those leaders will enable] people who have not understood [MET] [God’s truth] to understand it, and [they will enable] those who have not paid attention to [MET] [God’s truth] to pay attention to it.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 [Even] those who act very hastily will have good sense, and those who cannot speak well will speak fluently and clearly.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 [At that time], people who are foolish/unwise will no longer be (admired/looked up to), and scoundrels will no longer be respected.
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 Foolish people say things that are foolish, and they plan to do evil things. Their behavior is disgraceful, and they say things about Yahweh that are false. They do not give food to those who are hungry, and they do not give water to those who are thirsty.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 Scoundrels do things that are evil and that deceive people; they plan to do evil things; by telling lies [in court] they cause poor people to (have trouble/be convicted), even when what the poor [people] are requesting is fair/just.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 But honorable people plan to do honorable/good things, and they do the honorable/good things that they plan to do.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 You women [of Jerusalem] who think that you are very secure/safe and think that everything is going well, listen to [IDM] what I say!
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 One year from now, you who now (are not worried about anything/think that everything is going well) will tremble, because there will be no grapes for you to harvest and no [other] crops to harvest.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 [So] tremble [now], you women who are not worried about anything! Take off your [fancy] clothes and put rough sackcloth around your waists.
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 Beat/Hit your breasts to show that you are grieving about [what will happen in] your fertile fields and to your fruitful grapevines,
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 because [only] thorns and thistles will grow in your soil. Your houses where you had joyful parties and your city where you have been happy will be gone.
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 The [king’s] palace will be empty; there will be no people in the city that [now] is very noisy. Wild donkeys will walk around and flocks of sheep will eat grass in the empty forts and watchtowers.
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 [It will be like that] until God pours his Spirit out on us from heaven. [When that happens], the deserts will become fertile fields, and abundant crops will grow in those fertile fields.
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 People [PRS] will act/rule justly/fairly in those desert areas, and people will act/rule righteously in those fertile fields.
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 And the result of their acting righteously will be that there will be peace, the land will be tranquil/quiet, and people will be secure/safe forever.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 My people will live in their homes peacefully, and safely, and calmly, in places of rest.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 [Even if a severe] hailstorm knocks down [the trees in] the forest, and [all the buildings in] the city are blown down,
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Yahweh [will greatly] bless you; you will plant [seeds in fields] alongside the streams [and there will be abundant crops]. Your donkeys and cattle will easily find grass to eat.
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.