< Isaiah 29 >

1 [This is a message from Yahweh: ] Terrible things will happen to Jerusalem, the city where [King] David lived. You people continue to celebrate your festivals each year.
Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
2 But I will cause you to experience a great disaster, [and when that happens], people will weep and lament [very much]. Your city will become like [MET] an altar [to me] [where people are burned as sacrifices].
Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
3 I will cause your enemies [to come to your city]; they will surround it by [building] towers and putting in place other things with which to attack you.
Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
4 Then you will talk [as though you were] buried deep in the ground [DOU]; it will sound like someone whispering from under the ground, like [SIM] a ghost speaking from a grave.
Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
5 But, suddenly your enemies will be blown away like dust; their armies will disappear like [SIM] chaff that is blown away [by the wind]. [It will happen] very suddenly.
Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
6 The Commander of the armies of angels will come [to help you] with thunder and an earthquake and a very loud noise, with a strong wind and a big storm and a fire that will burn up everything.
Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
7 [Then] the armies of all the nations that will be attacking Jerusalem will quickly disappear like a dream in the night [DOU]. Those who will be attacking Jerusalem will suddenly vanish/disappear.
Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
8 People who are asleep dream about eating food, [but] when they wake up, they are still hungry. People who are thirsty dream about drinking something, [but] when they wake up they are still thirsty. It will be like that when your enemies come to attack Zion Hill; [they will dream about conquering you, but when they wake up, ] [they will realize that they have not succeeded].
kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
9 You [people of Jerusalem], be amazed and surprised [about this] [IRO]! Do not believe [what I have said] [SAR]! And continue to be blind [IRO] [about what Yahweh is doing]. You are stupid, but it is not because you have drunk a lot of wine. You stagger, but not from drinking alcoholic drinks.
Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
10 Because Yahweh has prevented the prophets [DOU] from understanding [and telling you his messages], [it is as though] he has caused you to be fast/deeply asleep.
Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
11 [Yahweh gave me] this vision; [but] for you, it is only words on a scroll that is sealed shut. If you give it to those who can read [and request that they read it], they will say, “We cannot read it because the scroll is sealed.”
Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
12 When you give it to [others] who cannot read, they will say, “[We cannot read it because] we do not know how to read.”
Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
13 [So] the Lord says, “These people say that they belong to me. They honor me by what they say [MTY], but they do not think [IDM] about what I [desire]. When they worship me, all they do is recite rules that people have made and that they have memorized.
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
14 Therefore, again I will do something to amaze these people; I will perform many miracles. And [I will show that] the people [who tell others that they] are wise are not really wise, and [I will show that] the people [who tell others that they] are intelligent are not really intelligent.
Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
15 Terrible things will happen to those who try to conceal from me, Yahweh, the [evil] things that they plan to do; they do those things in the darkness and they think, ‘Yahweh certainly cannot [RHQ] see us; he cannot [RHQ] know what we are doing!’
Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
16 They are extremely foolish! [They act as though] they were the potters and I was the clay! Something that was created should certainly never [RHQ] say to the one who made it, ‘You did not make me!’ A jar should never say, ‘The potter who made me did not know what he was doing!’”
Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
17 Soon [the forests in] Lebanon will become fertile fields, and abundant crops will grow in those fields, and that will happen very soon.
Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
18 At that time, deaf people will [be able to hear]; [they will be able to] hear when someone reads from a book; and blind people will [be able to see]; [they will be able to] see things when it is gloomy and [even] when it is dark.
A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
19 Yahweh will enable humble people to be very joyful again. Poor people will rejoice about what the Holy One of Israel [has done].
Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
20 There will be no more people who ridicule [others] and no more arrogant people. And those who plan to do evil things will be executed.
Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
21 Those who testify falsely in order to persuade judges to punish innocent people will vanish/disappear. Similar things will happen to those who by lying in court [persuade judges to] make unjust decisions.
waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
22 That is why Yahweh, who rescued Abraham, says about the people of Israel, “My people will no longer be ashamed; no longer will they show on their faces that they are ashamed.
Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
23 When they see that I have blessed them by giving them many children and doing many other things for them, they will realize that I am the Holy One of Israel, and they will revere me, the God to whom they, the descendants of Jacob, belong.
Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
24 When that happens, those who have not been able to think well will think clearly, and those who complain [about what I am doing] will accept what I am teaching them.”
Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”

< Isaiah 29 >