< Isaiah 23 >
1 [I received] this message [from Yahweh] about Tyre [city]: You [sailors on] [APO] ships from Tarshish, weep, because [the harbor of] Tyre and all the houses [in the city] have been destroyed. The reports that you heard in Cyprus [island] about Tyre [are true].
Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
2 You people who live along the coast [near Tyre], and merchants of Sidon [city], mourn silently. Your sailors went across the seas [to many places like Tyre].
Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
3 They sailed across deep seas to buy grain in Egypt and [other] crops that are grown along the Nile [River]. Tyre became the city where people from [all] nations bought and sold goods.
A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
4 But now you people in Sidon should be ashamed, because [you trusted in Tyre], which has been a strong fortress [on an island] in the sea. [Tyre is like a woman who is saying], “[Now it is as though] I have not given birth to [any] children, or raised [any] sons or daughters.”
Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
5 When [the people of] Egypt hear what has happened to Tyre, they will grieve very much.
Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
6 Sail to Tarshish [and tell them what happened]; weep, you people who live along the coast.
Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
7 [The people in] the very old city [of Tyre] were [RHQ] previously joyful. Traders [PRS] from Tyre established colonies in many distant nations.
Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
8 People from Tyre appointed kings [over other places]; their traders were wealthy; they were [as powerful and wealthy as] [MET] kings. [So], who [RHQ] caused the people of Tyre to experience this disaster?
Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
9 It was the Commander of the armies of angels who did it; he did it in order to cause [you people in] Tyre not to be proud any more, to humiliate you men who are honored all over the world.
Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
10 You people of Tarshish, you must grow crops in your land [instead of trading]; spread out over your land like [SIM] the Nile [River] spreads over the land [of Egypt] when it floods, because there is no harbor [in Tyre for your ships] now.
Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
11 [It is as though] Yahweh stretched out his hand over the sea and shook the kingdoms of the earth. He commanded that in Phoenicia/Canaan all its fortresses must be destroyed.
Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
12 He said to the people of Sidon, “You will never rejoice again, because you will be crushed; even if you flee to Cyprus [island], you will not escape destruction.”
Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
13 Think about what happened in Babylonia: the people who were in that land have disappeared. [The armies of] Assyria have caused that land to become a place where wild animals from the desert live. The Assyrians built dirt ramps to the top of the walls [of the city of Babylon]; [then they entered the city and] tore down the palaces and caused the city to become [a heap of] rubble.
Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
14 [So] wail, you [sailors on the] ships of Tarshish, because the harbor [in Tyre where your ships stop] is destroyed!
Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
15 For seventy years, which is as long as kings usually live, people will forget about Tyre. [But then it will be rebuilt]. What will happen there will be like what happened to a prostitute in this song:
A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
16 “You harlot, whom people had forgotten, play your harp well, and sing many songs, in order that people will remember you again.”
“Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
17 [It is true that] after seventy years Yahweh will restore Tyre. Their merchants will again earn a lot of money by buying things from and selling things to many [other] nations [HYP].
A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
18 [But] their profits will be given to Yahweh. [The merchants] will not hoard their money; instead, they will give it to Yahweh’s priests in order that they [can] buy food and nice clothes.
Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.