< Isaiah 13 >

1 [I], Isaiah, the son of Amoz, received [from Yahweh] this message about Babylon [city]:
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Lift up a flag on the bare [top of a] hill, to signal [that an army should come to attack Babylon]. Shout to them and wave your hand [to signal to them] that they should march through the city gates into the palaces of the proud [rulers of Babylon]!
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 [Yahweh says], “I have commanded those soldiers to do that; I have summoned the warriors whom I have chosen to punish [the people of Babylon] because of my being very angry with them, and those soldiers will be very proud [when they do that].”
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Listen to the noise on the mountains, which is the noise of a huge army marching! It is the noise made by people of many people-groups shouting. The Commander of the armies of angels has summoned this army to gather together.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 They come from countries that are far away, from the most remote places [IDM] on the earth. They are [like] [SIM] weapons that Yahweh will use [to punish the people with whom] he is very angry, and to destroy the entire country [of Babylonia].
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 [You people of Babylon] will scream because you will be terrified, because it will be the time that Yahweh [has determined/chosen], the time for the all-powerful [God] to destroy [your city].
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 All of your people will be very afraid [DOU], with the result that they will be unable even to lift their arms.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 All of you will be terrified. You will have [PRS] severe pains like [SIM] a woman has when she is giving birth to a baby. You will look at each other helplessly, and it will show on your faces that you feel horror.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Listen to this: The day that Yahweh has appointed/chosen is near, the day that he will furiously and fiercely [punish you] because he is very angry [with you]. He will cause your land [of Babylonia] to be desolate/barren, and he will destroy [all] the sinners in it.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 [When that happens], none of the stars will shine. When the sun rises, it will be dark, and there will be no light from the moon [at night].
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 [Yahweh says], “I will punish [everyone in] the world for the evil things that they do; I will punish the wicked people for the sins that they have committed. I will stop arrogant/proud people from being proud, and I will stop ruthless people from acting cruelly.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 [And because I will cause most people to die], people will be harder to find than gold, harder to find than fine gold from Ophir [in Arabia].
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 I will shake the sky, and the earth will [also] move out of its place. That will happen when [I], the Commander of the armies of angels, punish [wicked people], when [I show them that] I am extremely angry [with them].
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 And all [the foreigners in Babylon will run around] like [SIM] deer that are being hunted, like sheep that do not have a shepherd. They will try to find other people from their countries, and [then] they will escape [from Babylon] and return to their own countries.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Anyone who is captured [in Babylon] will be killed by [their enemies’] swords [DOU].
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Their little children will be dashed to pieces on the rocks while [their parents] watch; [their enemies] will steal everything valuable from their houses and will rape their wives.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Look! I am going to incite the people of Media to attack Babylon. The [army of Media] will attack Babylon, even if they are offered [DOU] silver or gold [if they promise to not attack it].
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 [With] their arrows, the [soldiers of Media] will shoot the young men [of Babylon]; they will not [even] act mercifully [DOU] toward infants or children!”
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 Babylon has been a very beautiful [MTY] city; [all] the people of Babylonia have been very proud of Babylon, [their capital city]; [but] God will destroy Babylon, like [SIM] he destroyed Sodom and Gomorrah.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 No one will ever live in Babylon again. It will be deserted forever. (Nomads/People who travel from place to place to live) will refuse to set up their tents there; shepherds will not bring their flocks of sheep to rest there.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Instead, animals that live in the desert will be there; jackals/wolves will live in [the ruins of] the houses. Owls (OR, Ostriches) will live in [the ruins], and wild goats will romp/jump around [there].
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Hyenas will howl in the [ruined] towers, and jackals/wolves will make their dens in [the ruins of] the palaces that [were previously] very beautiful. The time when [Babylon will be destroyed] is very near; Babylon will not exist much longer.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaiah 13 >