< Isaiah 12 >

1 At that time, you [people of Jerusalem] will sing [this song]: “Yahweh, we praise you! [Previously], you were angry with us, but you are not angry now and you have comforted us.
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
2 Amazingly, you [have come to] save us, [so] we will trust [in you] and not be afraid. Yahweh our God, you enable us to be strong; you are [the one about whom] we sing; you have rescued us [from our enemies].”
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
3 You(pl), [his people], will greatly enjoy being saved like [MET] you enjoy drinking water from a fountain.
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
4 At that time you [all] will say, “We should thank Yahweh! We should praise him [MTY]! We should tell [the people of all] the people-groups what he has done; we should enable them to know that he [MTY] is very great!
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
5 We should sing to Yahweh, because he has done wonderful things. We should enable everyone in the world to know it!
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
6 You people of Jerusalem, shout joyfully to praise Yahweh, because he is the great Holy One whom we Israeli [people worship], and he lives among us!”
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”

< Isaiah 12 >