< Hosea 10 >

1 “Israel was [like a large] healthy/luxuriant vine [MET] that produced [a lot of] grapes. But as the people became richer, they made more altars [at which to worship idols]. As the people prospered, they [built and] decorated sacred pillars [that they worshiped].
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 They are deceitful; [so] now they are guilty and must be punished. [I], Yahweh, will tear down their altars and smash those pillars.
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 Then they will say, ‘It is because we did not revere Yahweh that we no [longer] have a king. But [even if we had] a king, he certainly could not [RHQ] do anything to help us.’
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 They falsely promise [that they will do many things]; they solemnly promise and make agreements, but they do not do what they promise. So people accuse and sue [each other in the courts]; they are like [SIM] poisonous weeds [that grow] in a plowed field.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 The people who live in Samaria [city] are worried about [what may happen to the idol that resembles] a calf [that they set up] at Beth-Aven [town]. The people in Samaria will mourn, and the priests there will cry about it [if it is damaged or destroyed]. [Previously] they shouted joyfully about its being very great; but now it will not be great any more.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 It will be taken to Assyria to be a gift for the great King [of Assyria]. [So the people of] Israel will be disgraced, and they will be ashamed because [they trusted in] that idol.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 The King of Samaria [and the other people in Samaria] will be gone; they will be like [SIM] a twig [that floats away] on the surface of the water [and disappears].
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 The altars on the tops of hills [where the people worshiped idols] will be destroyed; those have been the places where the people of Israel sinned greatly. Thorns and weeds will grow and cover those altars. Then the people will plead to the mountains and hills, ‘Fall [down and] cover us [to protect us from God punishing us]!’
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 [You people of] Israel, [ever since your ancestors did evil things] at Gibeah, you have continued to sin. [When the people at] [PRS] Gibeah [did evil things], the result was a war [in which thousands of people died].
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 [So now], when I want to, I will punish the Israeli people. Because of the many sins that they have committed, [the armies of other] nations will gather to attack them, and they will cause the Israeli people to become their slaves.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Israel is [like] [MET] a well-trained (heifer/young cow) that likes to thresh [grain]. [So now you will become slaves]. [It will be as though] I will put a yoke on your neck, and you will be forced to work hard for your enemies in their fields. [You people of] Israel and Judah [will be forced to go to Assyria]; there you [DOU] will pull plows to break up the ground [for planting seeds].
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 [You plow your fields and plant your seeds] and harvest [your crops] [MET], [but what you need to do is] to act righteously and to faithfully love [me]; you need to repent [MET], because it is time to try to know [me], Yahweh; and if you do that, I will pour out [MET] many blessings on you.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 You [plant seeds and harvest the crops and eat them]; [but what I consider that you have really done is] that you have planted wicked things and harvested evil things and eaten [MET] the results [IDM] of the lies [that you have told]. [Instead of trusting in me, ] you have (depended on/trusted in) your own power and in your many soldiers.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 As a result, you will [soon] hear the roar of battle, and all your cities that have walls around them will be destroyed, like [SIM] Shalman’s [army] destroyed Beth-Arbel [city] in a battle, and the women [in that city] and their children were bashed to death.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 [You people of] [APO] Bethel [city], that is what will happen to you, because you are very wicked. And when the sun rises [on that day], the King of Israel will be killed [in the battle].”
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.

< Hosea 10 >