< Habakkuk 1 >

1 [I am] Habakkuk, a prophet. This is the [message that Yahweh] gave to me in a vision.
Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
2 [I said, ] “Yahweh, how long must I continue to call [to you] for help before you respond? I cry out to you [for help], saying that [people are acting] violently [everywhere], but you do not rescue us!
Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
3 (Must I/I do not want to) continue seeing people doing what is unjust [RHQ]. Why do you not punish people who are doing what is wrong [RHQ]? I see people destroying things and [acting] violently. There is fighting and quarreling [everywhere].
Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
4 No one obeys laws [PRS], and judges [PRS] never do what is fair/just. Wicked people always defeat righteous people [in the courts], with the result that matters are never decided fairly/justly.”
Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
5 [Yahweh replied to me, ] “[I know that what you say is true, but] look around at [what is happening in] the other nations; [if you look, ] you will be amazed, because I am doing something during this time that you would not believe [would happen], even if someone told you about it.
“Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
6 The soldiers of Babylonia are fierce/cruel and swift. And now I am causing them [to become very powerful]; they will march across the world and conquer [many] other countries.
Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
7 They are people whom [others] fear very much [DOU], and they do whatever they want to, paying no attention to the laws of other countries.
Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
8 The horses [that pull their chariots] go faster than leopards, and they are fiercer than wolves are in the evening. The horses on which the soldiers ride gallop swiftly; the soldiers riding them come from distant places. They are like [SIM] eagles that swoop down to [snatch and] kill small animals.
Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
9 As they ride along, [they are] determined to act violently. They advance like [SIM] a wind from the desert, gathering prisoners that are as [numerous as grains of] sand.
duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
10 They make fun of kings and princes [of other countries], and they ridicule all the cities that have high walls around them. They pile dirt [outside those walls] [in order to climb up] and capture those cities.
Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
11 They rush past like the wind, and then they go [to attack other cities]. But they are very guilty, because [they think that] their own power is their god.”
Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
12 [Then I said, ] “Yahweh, you have certainly [RHQ] always/forever been God. You are my Holy One; you will not die. So [why] have you appointed those men [from Babylonia] to judge and get rid of [us]? You are like [MET] a huge rock [under which we are protected/safe], so why have you sent them to punish us?
Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
13 You [SYN] are pure, and you cannot endure looking at what is evil, [so why] are you ignoring men who are treacherous? Why do you do nothing [to punish] those wicked men [from Babylonia] who destroy people who are more righteous than they [are]?
Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
14 [Do you consider that] we are like fish in the sea, or like other creatures in the sea, that have no ruler?
Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
15 [The soldiers of Babylonia think that we are fish] [RHQ] for them to pull out of the sea with hooks or to catch in their nets, while they rejoice and celebrate.
Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
16 If they catch us, they will [worship] their weapons [MET] with which they captured us, and offer sacrifices to them and burn incense in front of them! [They will say] ‘Those weapons have enabled us to become rich and be able to eat expensive food.’
Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
17 [Will you allow] them to continue [to conquer people] [MET] forever? [Will you allow] them to destroy people of other nations without their being merciful [to anyone]?”
Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?

< Habakkuk 1 >