< Genesis 49 >
1 Jacob summoned all his sons, and said to them,
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 “Gather around me in order that I can tell you what will happen in the future. My sons, come and listen to me. I am your father, [Jacob, whom God named] Israel.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 Reuben, you are my oldest son. You were born when I was young and energetic/strong. You are prouder and stronger than all the rest of my sons.
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 But you were as uncontrollable as a flood [SIM]. So now you will not be my most important son, because you climbed up onto my bed, and had sex with [MTY] my (concubine/slave who had become one of my wives). Your doing that caused me, your father, to have great shame.
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 Simeon and Levi, you have both acted like criminals. You use your swords to act violently.
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 I do not want to be with you when you make evil plans [DOU]. I do not want to join you in your meetings, because you killed people when you became very angry, and you (hamstrung/cut the tendons in the legs of) oxen just to (have fun/see them suffer).
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 God says, ‘I will (curse/cause bad things to happen to) them for being very angry, for acting very cruelly when they were very furious. I will scatter their descendants [MTY] throughout Israel land.’
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Judah, your [older and younger] brothers will praise you. They will bow down before you, because you will thoroughly defeat [MTY] your enemies.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 Judah is like a young lion [SIM] that has returned to its den satisfied after eating the animals that it has killed. He is like a lion that lies down and stretches out after eating; no one would dare to disturb it [RHQ].
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 There will always be a ruler [MTY] from the descendants of Judah [MTY]. Each one will hold a scepter/staff to show that he has authority as a king. He will do that until the one to whom the scepter belongs comes, the one to whom the nations will bring tribute and show that they will obey him.
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 The grapevines of Judah’s descendants will produce grapes very abundantly. As a result, they will not object to tying their young donkeys to the grapevines in order that the donkeys can eat the leaves of the grapevines. [Wine will be very plentiful, with the result that] they could wash their cloaks in wine that is as red as blood [MET].
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 Their eyes will be red because of [drinking too much] wine, but their teeth will be very white because of drinking much milk [from the cows].
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 Zebulun, your descendants will live by the seashore where there will be a safe harbor for ships. Their land will extend north as far as Sidon [city].
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 Issachar, your descendants will be like strong donkeys that are lying down on the ground between their loads, [so tired that they cannot get up]!
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 They will see that their resting place is good, and that the land pleases them very much. But they will bend their backs to carry heavy loads and be forced to work for others.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 Dan, although your tribe will be small, their leaders will rule their people just like the leaders of other tribes of Israel will rule their people.
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Your descendants will be like snakes at the side of a road, like poisonous snakes lying beside a path. They will strike the heels of horses that pass by, causing the riders to fall backwards [as the horses rear up on their hind legs].”
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 Then Jacob prayed, “Yahweh, I am waiting for you to rescue me [from my enemies].”
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 [Then Jacob continued telling his sons what would happen in the future. He said], “Gad, your tribe/descendants will be attacked by a group of bandits, but your tribe/descendants will pursue and attack them [MTY].
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 Asher, your descendants will eat good-tasting food; they will produce food that is delicious enough for kings to eat.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 Naphtali, your descendants will be like deer [MET] that are (free to/not tied down and can) run wherever they wish. They will give birth to children who are good-looking like (fawns/baby deer) [MET].
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 Joseph, you will have many descendants [MET]. Their children will be as many as the fruit on a vine near a spring of water, whose branches extend over a wall.
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 Their enemies will attack them fiercely, and shoot at them with bows and arrows and pursue them.
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 But they will hold their bows steady and their arms will remain strong, because of the power [MTY] of my mighty God, because of Yahweh who guides and provides for me [MET] like a shepherd guides and provides for his sheep. The people of Israel will [ask Yahweh to protect them], [like people hide under] a huge [overhanging] to be protected.
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 God, the one whom I worship, will help your descendants. God Almighty will bless them by sending them rain from the sky and by giving them water from deep/far below the ground. He will give them many cattle and children [MET] (OR, and their cattle will have many offspring).
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 The blessings that I want God to give you are great ones. They are greater than the blessings that come from the eternal mountains, greater than the ones that come from the everlasting hills. Joseph, I pray that these blessings will (be given to you/come upon your head), because you are the leader of your [older] brothers [and younger brother].
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 Benjamin, your descendants will be like [MET] vicious/fierce wolves: In the morning they will kill their enemies like a wolf devours (its prey/the animals that it has killed), and in the evening they will divide among their warriors the spoils that they seized from their enemies.”
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 Those twelve sons are the ancestors of the twelve tribes of Israel. That is what their father said to them as he blessed them, telling to each one words that were appropriate for him.
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 Then Jacob said to his sons, “I will soon die. Bury my body where some of my ancestors are buried, in the cave that is in the field that was bought from Ephron, who belonged to the Heth people-group.
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 That field is in the Machpelah area, east of Mamre [town], in Canaan. My grandfather Abraham bought it from Ephron to use as a burial place.
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 That is where they buried him and his wife Sarah. That is where they buried my father Isaac and his wife Rebekah. And that is where I buried my wife Leah.
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
32 That field and the cave in it were bought from the Heth people-group; so that is where I want you to bury me.”
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 When Jacob finished giving those instructions to his sons, he lay down on his bed again. Then he died [IDM].
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.