< Genesis 47 >

1 Joseph chose five of his [older] brothers to go with him to talk to the king. He introduced his [older] brothers to the king, and then he said, “My father and my [older] brothers [and younger brother] have come from the Canaan region. They have brought all their sheep and goats and cattle and everything else that they own, and they are living now in Goshen region.”
Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
2
Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
3 The king asked the brothers, “What work do you do?” They replied, “We are shepherds, just as our ancestors were.”
Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
4 They also said to him, “We have come here to live for a while in this land, because the famine is very severe in Canaan, and our animals have no (pasture/grass to eat) there. So now, please let us live in the Goshen region.”
Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
5 The king said to Joseph, “I am happy that your father and your [older] brothers [and younger brother] have come to you.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
6 They can live wherever you want in the whole country of Egypt. Give your father and your brothers the best part of the land. They can live in Goshen. And if you know that any of them have any special ability to work with livestock, have them be in charge of my own livestock, too.”
ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
7 Then Joseph brought his father Jacob [into the palace] and introduced him to the king. Jacob asked God to bless the king.
Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
8 Then the king asked Jacob, “How old are you?”
sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
9 Jacob replied, “I have been traveling around for 130 years. I have not lived as long as my ancestors, but my life has been full of troubles.”
Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
10 Then Jacob again [asked God to] bless the king, and left him.
Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
11 [That is how Joseph enabled his father and older] brothers [and younger brother] to start living in Egypt. As the king had commanded, he gave them property in the best part of the land, in [Goshen, which is now called] Rameses.
Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
12 Joseph also provided food for all his father’s family. The amounts that he gave them were according to how many children each of them had.
Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
13 There were no crops growing in the whole region, because the famine was very severe. The people of Egypt and Canaan [MTY] became weak because they did not have enough food to eat.
A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
14 Joseph collected all the money that the people in Egypt and Canaan paid for the grain they were buying from him, and he brought the money to the king’s palace.
Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
15 When the people of Egypt and Canaan had spent all their money for grain, they all kept coming to Joseph and saying, “Please give us some food! If you do not give us grain, we will die [RHQ]! We have used all our money to buy food, and we have no money left!”
Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
16 Joseph replied, “Since your money is all gone, bring me your livestock. If you do that, I will give you food in exchange for your livestock.”
Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
17 So they brought their livestock to Joseph. He gave them food in exchange for their horses, their sheep and goats, their cattle, and their donkeys.
Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
18 The next year they came to him again and said, “We cannot hide this from you: We have no more money, and now our livestock belongs to you. We have only our bodies and our land to give to you. We have nothing else left.
Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
19 (If you do not give us some food, we will die!/Do you want to watch us die?) [RHQ] If you do not give us seeds, our fields will become useless [IDM]. Buy us and our land in exchange for food. Then we will be the king’s slaves, and he will own the land. Give us seeds that we can plant and grow food, in order that we will not die, and in order that our land will not become like a desert.”
Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
20 So Joseph bought all the farms in Egypt for the king. The people of Egypt each sold their land to him because the famine was very severe, [and they had no other way to get money to buy food]. So all the farms became the king’s farms.
Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
21 As a result, Joseph caused all the people from one border of the country to the other to become the king’s slaves.
Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
22 But he did not buy the priests’ land, because they received food from the king regularly, so the food that the king gave them was enough for them. That is the reason they did not sell their land to him.
Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
23 Joseph said to the people [who sold themselves and their land to him], “Listen to me! Today I have bought you and your land for the king. So here are seeds for you so that you can plant them in the ground.
Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
24 But when you harvest the crop, you must give one-fifth of the crop to the king. The rest of the crop you can keep, to be seed to plant in the fields, and to be food for you and your children and for everyone else in your household to eat.”
Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
25 They replied, “You have saved our lives! We want you to be pleased with us. And we will be the king’s slaves.”
Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
26 So Joseph made a law about all the land in Egypt, stating that one-fifth of the crops that are harvested belongs to the king. That law still exists. Only the land that belonged to the priests did not become the king’s land.
Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
27 Jacob and his family started to live in Egypt, in the Goshen region. They acquired property there. Many children were born to them there. As a result, their population increased greatly.
To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
28 Jacob lived in Egypt 17 years. Altogether he lived 147 years.
Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
29 When it was almost time for him to die, he summoned his son Joseph and said to him, “If I have pleased you, make a solemn promise that you will be kind to me and faithfully do what I am now asking you: When I die, do not bury me here in Egypt.
Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
30 Instead, take my body out of Egypt, and bury it in Canaan where my ancestors are buried.” Joseph replied, “I will do that.”
amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
31 Jacob said, “(Swear/Solemnly promise) to me that you will do it!” So Joseph swore to do it. Then Jacob turned over in bed, bowed his head, and worshiped God.
Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.

< Genesis 47 >