< Genesis 4 >

1 Adam (had sex/slept) with his wife Eve, and she became pregnant and gave birth to a son whom she named Cain, [which sounds like the word that means ‘produce’], because, she said, “By Yahweh’s help I have produced a son.” Some time later she gave birth to another son, and she named him Abel.
Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
2 [After those boys grew up], Abel (tended/took care of) sheep and goats, and Cain became a farmer.
Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
3 One day Cain harvested some of the crops he had grown and brought them to Yahweh as a gift for him,
Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
4 and Abel took from his flock some of the first lambs that had been born [and killed them] and, as a gift, gave to Yahweh the fatty parts, [which were the best parts]. Yahweh was pleased with Abel and his offering,
Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
5 but he was not pleased with Cain and his offering. So Cain became very angry, and his face looked dejected.
amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
6 Yahweh said to Cain, “(You should not be angry!/Why are you angry?) [RHQ] (You should not scowl like that!/Why do you scowl like that?) [RHQ]
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
7 If you had done what was right (OR, if you do what is right) [RHQ], I would accept your offering. But if you do not do what is right, [your desire to] sin [is ready to attack you like a wild animal that] [PRS] crouches outside the doorway, [ready to spring on its victim] [MET]. [Your desire to] sin wants to control you, but you must (control/not obey) it.”
Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
8 But one day, Cain said to his younger brother Abel, “Let’s go for a walk in the fields.” [So they went together]. And when they were in the countryside, suddenly Cain attacked Abel and killed him.
To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
9 [Later, even though] Yahweh [knew what Cain had done], he said to Cain, “[Do you know] where Abel, your younger brother, is?” Cain replied, “No, I do not know. (My job is not to guard my younger brother!/Am I supposed to take care of my younger brother?)” [RHQ]
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
10 Yahweh said, “You have done a terrible thing [RHQ]! So now [it is as though] your younger brother’s voice is crying to me from the ground, demanding that his death must be avenged.
Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
11 You have killed your younger brother, and the ground has soaked up his blood. So now I will expel you from this land and curse your efforts to produce crops.
Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
12 You will till the ground to plant crops, but the ground will produce very few [HYP] crops. And you will continually wander around the earth, and not have any place to live permanently.”
In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
13 Cain replied, “You are punishing me more then I can endure.
Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
14 You are about to expel me from the ground [that I have been cultivating], and I will no longer be able to come (into your presence/and talk with you). Furthermore, I will be continually wandering around the earth with no place to live permanently, and anyone who sees me will kill me.”
Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
15 But Yahweh said to him, “No, that will not happen. I will put a mark on you to warn anyone who sees you that [I will punish him severely if] he kills you. I will punish that person seven times as severely as I am punishing you.” Then Yahweh put a mark on Cain’s forehead.
Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
16 So Cain left Yahweh and went to live in the land called Nod, [which means ‘wandering’], which was east of Eden.
Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
17 Some time later, Cain (had sex/slept) with his wife, and she [became pregnant and] gave birth to a son, whom she named Enoch. Then Cain started to build a city, and he named the city ‘Enoch’, the same name that his son had.
Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
18 Enoch [grew up and married and] became the father of a son whom he named Irad. When Irad [grew up he] became the father of a son whom he named Mehujael. Mehujael [grew up and] became the father of a son whom he named Methuselah. Methuselah [grew up and] became the father of Lamech.
Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
19 When Lamech [grew up he] married two women. The name of one was Adah and the other was Zillah.
Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
20 Adah gave birth to [a son she named] Jabal.
Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
21 Later, Jabal was the first person who lived in tents because he traveled from place to place to take care of livestock. His younger brother’s name was Jubal. He was the first person who made/played a (lyre/stringed instrument) and a flute.
Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
22 [Lamech’s other wife] Zillah gave birth to a son whom she named Tubal-Cain. Later Tubal-Cain became a (blacksmith/one who made tools from bronze and iron). Tubal-Cain had a younger sister whose name was Naamah.
Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
23 One day Lamech said to his two wives, “Adah and Zillah, listen carefully to what I am saying. A young man struck me and wounded me, so I killed him.
Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
24 Yahweh said long ago that he would avenge and punish anyone who killed Cain seven times as much as he punished Cain [for killing his younger brother]. So if anyone [tries to] kill me, I will punish him 77 times as much [as Yahweh punished Cain].”
Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
25 Adam continued to (have sex/sleep) with [EUP] his wife, and she [became pregnant and] gave birth to another son, whom she named Seth, [which sounds like the Hebrew word that means ‘given’], because, she said, “God has given me another child to take the place of Abel, since Cain killed him.”
Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
26 When Seth grew up, he became the father of a son whom he named Enosh. About that time people began to worship Yahweh [again].
Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.

< Genesis 4 >