< Genesis 39 >

1 Meanwhile, the descendants of Ishmael took Joseph down to Egypt. There Potiphar bought Joseph from them. Potiphar was an Egyptian who was one of the king’s officials and the captain of the king’s (palace guards/guards who protected the king).
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 Because Yahweh helped Joseph, he was able to do his work very well, and lived in the house of his Egyptian master.
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 His master saw that Yahweh was helping Joseph and enabling him to be successful in everything that he did.
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 Joseph’s master was pleased with him, so he appointed him to be his personal servant. Then he appointed him to be the one who would take care of everything in his household and all of his possessions.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 From the time Potiphar appointed Joseph to take care of everything in his household and all that he owned, Yahweh blessed the people who lived in Potiphar’s house because of Joseph. He also caused Potiphar’s crops to grow well.
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 Potiphar allowed Joseph to take care of everything that he owned. Potiphar needed to decide only about the food he ate. He was not concerned about anything else in his house. Joseph was well-built/muscular and handsome.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 Because of that, after a while, his master’s wife started to look fondly at Joseph. So one day she said to him, “Have sex [EUP] with me!”
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 But he refused, saying to his master’s wife, “Listen! My master is not concerned about anything in this house. He has appointed me to take care of everything that he owns.
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 No one in this household has more authority than I do. The only thing that he has not allowed me to have is you, because you are his wife! So (how could I do this wicked thing [that you are asking me to do]?/I certainly could not do this wicked thing!) [RHQ] I would be sinning against God if I did that!”
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 She kept on asking Joseph day after day to have sex [EUP] with her, but he refused. He would not even go near her.
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 One day Joseph went into the house to do his work, and none of the other household servants were in the house.
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 Potiphar’s wife grabbed his cloak and said, “Have sex [EUP] with me!” Joseph ran out of the house, but his cloak was still in her hand!
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 When she saw that he had run outside leaving his cloak in her hand,
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 she called the household servants. She said to them, “Look! This Hebrew man that my husband brought to us is (insulting/trying to do something disgraceful to) us! He came into my room and tried to (rape me/make me have sex [EUP] with him), but I screamed loudly.
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 As soon as he heard me scream loudly, he left his loincloth with me and ran outside!”
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 She kept the loincloth beside her until her husband, Joseph’s master, came home.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 Then she told him this story: “That Hebrew slave whom you brought here came into my room and tried to rape me!
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 As soon as I screamed loudly, he ran outside, leaving me holding his loincloth!”
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 When Joseph’s master heard this story that his wife told him, saying “This is how your slave treated me,” he was very angry.
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 Joseph’s master took Joseph and put him in prison, the place where all the king’s prisoners were put, and Joseph stayed there.
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 But Yahweh was kind to Joseph and helped him, and caused the (prison warden/man who was in charge of the prison) to be pleased with him.
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 So the prison warden put Joseph in charge of all those who were in the prison, and in charge of all the work that was done there.
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 The warden was not concerned with anything that Joseph was taking care of, because Yahweh helped Joseph to do well everything that he did.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.

< Genesis 39 >