< Genesis 38 >

1 At that time, Judah left his older and younger brothers and went down from the hilly area and stayed with a man whose name was Hiram, who lived in Adullam [town].
A wannan lokaci, Yahuda ya bar’yan’uwansa ya gangara don yă zauna da mutumin Adullam, mai suna Hira.
2 There he (met/became acquainted with) a woman who was the daughter of a man from Canaan named Shua. He married her. He had sex [EUP] with her,
A can Yahuda ya sadu da’yar wani Bakan’ane, mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya kuma kwana da ita;
3 and she became pregnant and later gave birth to a son, whom he named Er.
ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er.
4 Later she became pregnant again and gave birth to another son whom she named Onan.
Ta sāke yin ciki, ta haifi wani ɗa, ta kira shi Onan.
5 Many years later, when Judah and his family went to live in Kezib [town], Judah’s wife gave birth to another son, whom she named Shelah.
Ta kuma haifi wani ɗa har yanzu, aka kuwa ba shi suna Shela. A Kezib ne ta haife shi.
6 When Judah’s oldest son Er [grew up], Judah got a wife for him, a woman named Tamar.
Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar.
7 But Er did something that Yahweh considered to be very wicked, so Yahweh caused him to die.
Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
8 Then Judah said to Onan, “Your older brother died without having any sons. So marry his widow and have sex [EUP] with her. That is what our customs require that you should do.”
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Onan, “Ka kwana da matar ɗan’uwanka ka cika wajibinka gare ta a matsayin ɗan’uwan miji, don ka samar wa ɗan’uwanka’ya’ya.”
9 But Onan knew if he did that, any children who would be born would not be considered to be his. So every time he had sex [EUP] with his brother’s widow, he spilled his semen on the ground, so that she would not get pregnant and produce children for his older brother.
Amma Onan ya san cewa’ya’yan ba za su zama nasa ba; saboda haka a duk sa’ad da ya kwana da matar ɗan’uwansa, sai yă zub da maniyyinsa a ƙasa don kada yă samar wa ɗan’uwansa’ya’ya.
10 Yahweh considered that what he did was wicked, so he caused him to die also.
Abin nan da ya yi mugunta ce a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi, shi ma.
11 Then Judah said to his daughter-in-law Tamar, “Return to your father’s house, but do not marry anyone else. When my youngest son Shelah grows up, [he can marry you].” But Judah [really did not want Shelah to marry her, because] he was afraid that then Shelah would die too, just as his older brothers had died. So Tamar [obeyed Judah and] went back to live in her father’s house again.
Sai Yahuda ya ce wa surukarsa Tamar, “Ki yi zama kamar gwauruwa a gidan mahaifinki sai ɗana Shela ya yi girma.” Gama ya yi tunani, “Shi ma zai mutu, kamar’yan’uwansa.” Saboda haka Tamar ta je ta zauna a gidan mahaifinta.
12 Several years later, Judah’s wife, who was the daughter of Shua, died. When the time of mourning for her was finished, Judah decided to go up to Timnah, to the place where his (men were shearing his sheep/sheep were being sheared) His friend Hiram, from Adullam, went with him.
Bayan an daɗe sai matar Yahuda,’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
13 Someone said to Tamar, “Your father-in-law is going to [the fields near the city of] Timnah to help the men who are shearing his sheep.”
Sa’ad da aka faɗa wa Tamar cewa, “Surukinki yana kan hanyarsa zuwa Timna don askin tumakinsa,”
14 [She realized that now Shelah was grown up, but Judah had not given her to him to be his wife. So] she took off her widow’s clothes, and covered her head with a veil, so that people would not (recognize her/know who she was). Then she sat down at the entrance to Enaim [town], which is on the road to Timnah.
sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba.
15 When Judah came along and saw her, he thought that she was a prostitute, because she had covered her head [like prostitutes often did] (OR, [and sat where prostitutes often sat)].
Sa’ad da Yahuda ya gan ta, ya yi tsammani karuwa ce, gama ta lulluɓe fuskarta.
16 Judah did not realize that she was his daughter-in-law. So he said to her, “Hey, let me have sex [EUP] with you!” She replied, “What will you give me for allowing you to have sex [EUP] with me?”
Bai san cewa ita surukarsa ce ba, sai ya ratse zuwa wurinta a gefen hanya ya ce, “Zo mana, in kwana da ke.” Sai ta ce, “Me za ka ba ni in na kwana da kai?”
17 He replied, “I will send you a young goat from my flock of goats.” She asked, “Will you give me something now for me to keep until you send the goat?”
Ya ce, “Zan aika miki da ɗan akuya daga garkena.” Sai ta ce, “Za ka ba ni wani abu jingina, kafin ka aika da shi?”
18 He replied, “What do you want me to give to you?” She replied, “Give me the ring that has your name on it that is tied by a cord around your neck, and give me the walking stick that you are holding in your hand.” So he gave them to her. Then he had sex [EUP] with her, and she became pregnant.
Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
19 After she left, she took off the veil and put her widow’s clothes on again.
Bayan ta tafi, sai ta tuɓe lulluɓin, ta sāke sa tufafin gwaurancinta.
20 Judah gave a young goat to his friend from Adullam, for him to take back to the woman, as he had promised. But his friend could not find the woman.
Ana cikin haka sai Yahuda ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa mutumin Adullam don yă karɓo masa jinginar daga wurin macen, amma bai same ta a can ba.
21 So he asked the men who lived there, “Where is the prostitute who was sitting by the road at Enaim?” They replied, “There has never been a prostitute here!”
Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.”
22 So he went back to Judah and said, “I did not find her. [Furthermore], the men who live in that town said, ‘There has never been a prostitute here.’”
Saboda haka sai ya koma zuwa wurin Yahuda ya ce, “Ban same ta ba. Ban da haka ma, mutanen da suke zama a can, sun ce, ‘Ba a taɓa kasance da wata karuwar haikali a nan ba.’”
23 Judah said, “She can keep the things that I gave to her. If we continued to search for her, people would ridicule us. I tried to send this young goat to her, but you could not find her to give it to her.”
Sa’an nan Yahuda ya ce, “Bari tă riƙe kayan kiɗa garin nema mu zama abin dariya. Ni kam, na aika da tunkiyar amma ba a same ta ba.”
24 About three months later, someone told Judah, “Your daughter-in-law Tamar has become a prostitute and now she is pregnant!” Judah said, “Drag her outside of the city and kill her by burning her!”
Bayan misalin wata uku sai aka faɗa wa Yahuda cewa, “Tamar, surukarka ta yi laifin karuwanci, a sakamakon haka yanzu ta yi ciki.” Yahuda ya ce, “A fid da ita, a ƙone!”
25 But as they were taking her outside of the city, she gave the ring and walking stick to someone, and told him to take them to Judah, and say to him, “The man who owns these things is the one who caused me to become pregnant.” She also said to tell him, “Look at this ring, and the cord that is attached to it, and this walking stick. Whose are they?”
Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
26 When the man did that, Judah recognized the ring and the stick. He said, “She is more righteous than I am. I did not tell my son Shelah to marry her, as I promised that I would.” And Judah did not have sex [EUP] with her again.
Yahuda ya gane su, sai ya ce, “Ai, ta fi ni gaskiya, da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Bai kuwa ƙara kwana da ita ba.
27 When it was time for her to give birth, [she was surprised that] there were twin boys in her womb.
Sa’ad da lokaci ya yi da za tă haihu, ashe, tagwaye’yan maza ne suke cikinta.
28 As she was giving birth, one of them put out his hand. So the midwife fastened a scarlet thread around his wrist, saying, “This one came out first.”
Yayinda take haihuwa, ɗaya daga cikinsu ya fid da hannunsa; sai ungonzomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, ta ce, “Wannan ne ya fito da farko.”
29 But he pulled his hand back inside the womb, and his brother came out first. So she said, “So this is how you break your way out first!” So she named him Perez, [which sounds like the Hebrew word that means ‘breaking out].’
Amma sa’ad da ya janye hannunsa, sai ɗan’uwansa ya fito, sai ta ce, “Wato, haka ne ka keta ka fito!” Sai aka ba shi suna Ferez.
30 Then his younger brother, the one who had the scarlet thread around his wrist, came out. And he was named Zerah, [which sounds like the Hebrew word that means ‘redness of dawn].’
Sa’an nan ɗan’uwansa wanda yake da jan zare a hannunsa ya fito, aka kuma ba shi suna Zera.

< Genesis 38 >