< Genesis 34 >

1 One day Dinah, the daughter of Jacob and Leah, went to visit some of the women in that area.
To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
2 Shechem, one of the sons of Hamor, the ruler of that area who was descended from the Hiv people-group, saw her. He wanted her. So he grabbed her and forced her to have sex [EUP] with him.
Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
3 He [SYN] was very much attracted to her, and fell in love with her, and he tried to get her to love him.
Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
4 So Shechem said to his father Hamor, “Please get this girl for me. I want her to become my wife!”
Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
5 Jacob very soon found out that his daughter Dinah had been disgraced/defiled. But his sons were in the fields with his livestock, so he did nothing about it until they returned home.
Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
6 In the meantime, Shechem’s father Hamor went to talk with Jacob.
Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
7 While they were still talking, Jacob’s sons came in from the field. When they found out what had happened, they were shocked and very angry. They said, “Shechem has done something that is very disgraceful among us Israeli people, something that never should be done!”
Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
8 But Hamor said to them, “My son Shechem really likes this girl. Please allow him to marry her.
Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
9 Let’s make an agreement: You will give your daughters to our young men to be their wives, and we will give our daughters to your young men to be their wives.
Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
10 You can live among us, and live anywhere in our land that you wish. You can buy and sell things (OR, travel around) and if you find land that you want, then you can buy it.”
Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
11 Then Shechem said to Dinah’s father and brothers, “If you feel good toward me and do what I am asking for, I will give you whatever you ask for.
Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
12 Tell me what gifts you want and what bride price you want, and I will give you what you ask for. I just want you to give the girl to me to be my wife.”
Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
13 But because Shechem had done a shameful thing to their sister Dinah, the sons of Jacob deceived Shechem and his father Hamor
Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
14 by saying to them, “No, we cannot do that. We cannot give our sister to be the wife of a man who is not circumcised, because that would be a shameful thing for us to do.
Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
15 We will do that only if you do one thing: You must become like us by circumcising all the males that are among you.
Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
16 Then we will give our daughters to your young men to be your wives, and we will take your daughters to be the wives of our young men. We will live among you, and we will become one people-group.
Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
17 But if you will not agree to being circumcised, we will take our sister and go back to our land.”
Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
18 What they said pleased Hamor and his son Shechem.
Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
19 Shechem was very much in love with Jacob’s daughter, so he quickly agreed to do what they suggested.
Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
20 Shechem went with Hamor to the meeting place near the city gate, and they spoke to the city leaders, saying,
Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
21 “These men are friendly toward us. We should let them live here and travel around (OR, buy and sell things) and if they find land that they want, they can buy it. There is plenty of land for them to live here. Our young men can marry their daughters, and their young men can marry our daughters.
Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
22 But these men will agree to live among us and become one people-group with us only if all our males are circumcised, as they are.
Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
23 But if we do that, just think! Their livestock and their possessions and their other animals will become ours [RHQ]! So we should agree to do what they suggest, and then they will live among us!”
Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
24 Shechem was the most respected person in his father’s household, so all the men who were there at the city gate agreed to what Hamor and Shechem suggested. So every male in the city was circumcised.
Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
25 On the third day after that, when the men of the city were still sore because of being circumcised, two of Jacob’s sons, Simeon and Levi, who were Dinah’s brothers, took their swords and entered the city without anyone opposing them, and killed all the men.
Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
26 They even killed Hamor and his son Shechem. Then they took Dinah out of Shechem’s house and left the city.
Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
27 Then the other sons of Jacob went into the city where all those dead bodies were. They (looted/took everything in) the city to get revenge for the shameful thing that had been done to their sister.
Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
28 They took away the people’s sheep and goats, their cattle, their donkeys, and everything else that they wanted from inside the city and from out in the countryside.
Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
29 They took away everything that was valuable, even the children and the women. They seized and took away everything that was in the houses.
Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
30 Then Jacob said to Simeon and Levi, “You have caused a lot of trouble for me! Now the Canaan people-group and the Perizzi people-group and everyone else who lives in this land will (hate me/say my name stinks)! I do not have many men to fight for us, so if they all gather together and come to me and attack us, they will destroy us and all our household!”
Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
31 But they replied, “(Should we have allowed Shechem to treat our sister like a prostitute?/We could not just let Shechem treat our sister like a prostitute!)” [RHQ]
Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”

< Genesis 34 >