< Genesis 31 >

1 Someone told Jacob that Laban’s sons were complaining and saying, “Jacob has become very rich by taking everything [HYP] that belonged to our father.”
Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
2 And Jacob noticed that Laban was not acting friendly toward him as he had done before.
Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
3 Then Yahweh said to Jacob, “Go back to your country and your relatives, and I will help you there.”
Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
4 So Jacob sent a message to Rachel and Leah, telling them to come out to the pastures where his flocks of sheep and goats were.
Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
5 When they arrived, he said to them, “I see that your father does not act friendly toward me as he did previously. But God, whom my father worshiped, has helped me.
Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
6 You two know that I have worked very hard for your father,
Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
7 but many times [HYP] he has cheated me by decreasing my wages. But God has not allowed him to harm me.
duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
8 When Laban said, ‘The speckled animals are the ones that I will give you to be your wages,’ then all the animals gave birth to young ones that were speckled. When he changed and said, ‘The ones that have black and white stripes on them will be your wages,’ then all the animals gave birth to young ones that were striped.
In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
9 In that way, God has taken away the livestock that belonged to your father and has given them to me.
Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
10 “One time, when the animals were mating, I had a dream. In my dream I [looked up and was surprised to] see that some of the male goats that were mating with the female goats had black and white stripes on them, some were speckled, and some were spotted.
“A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
11 An angel who was sent by God said to me in the dream, ‘Jacob!’ I replied, ‘I am here!’
Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
12 He said to me, ‘Look up and you will see that all the male goats that are mating have black and white stripes on them, or are speckled or spotted. This is happening because I have seen all that Laban has done to you.
Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
13 I am God who appeared to you at Bethel, where you set up a stone to show that the place was holy, and you poured [olive] oil on the stone and made a solemn promise to me. So now leave this land immediately, and return to the land where you were born.’”
Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
14 Rachel and Leah replied, “Our father will not give us anything more when he dies [RHQ].
Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
15 He treats us as though we were foreigners [RHQ]! [Your working for him all these years was like a payment] that you gave him as a price for us, but we will not inherit any of that money that he got as a price for us. He has spent it all!
Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
16 Surely all of the wealth that God took away from our father belongs to us and to our children. So do whatever God has told you to do!”
Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
17 Then Jacob put his children and his wives on camels.
Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
18 He made all his livestock go ahead of him. Besides the livestock, he took along all the other things that he had acquired while living in Paddan-Aram. And they prepared to return to his father Isaac, in the Canaan region.
ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
19 Before they left, while Laban was shearing his sheep, Rachel stole the [small wooden] idols [that were in her father’s tent].
Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
20 Furthermore, Jacob deceived Laban, who belonged to the Aram people-group, by not telling him that they were planning to leave.
Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
21 So Jacob and his family fled with all their possessions, and they crossed the Euphrates River, and then started traveling south toward the hilly Gilead region.
Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
22 On the third day after they left, someone told Laban that Jacob and his family had left.
A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
23 So he took some of his relatives with him and started to pursue Jacob. They continued walking for seven days.
Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
24 Then God appeared to Laban in a dream at night, and said to him, “When you catch up to Jacob, be sure that you do not say anything at all [HYP] to him in an angry manner!”
Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
25 The next day, by the time Laban caught up with Jacob, Jacob and his household had set up their tents in the hilly Gilead region. So Laban and his relatives set up their tents there, too.
Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
26 Then Laban went to Jacob and said to him, “Why have you done this? You have deceived me by carrying away my daughters as though you had captured them in a war [MTY]!
Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
27 Why did you run away and deceive me? Why did you not tell me that you were going to leave, so that we could have rejoiced and sung while people played music on tambourines and harps before I said ‘goodbye’ to you?
Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
28 (You did not even let me kiss my grandchildren and my daughters goodbye before they left!/Why did you not allow me to kiss my grandchildren and daughters goodbye before they left?) [RHQ] What you have done was foolish!
Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
29 My relatives and I have the power to harm you, but last night the God whom your father worships said to me in a dream, ‘Be sure that you do not say anything at all to Jacob in an angry way.’
Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
30 Now, I know you have left because you long to go back home. But why did you steal my [wooden] idols?”
Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
31 Jacob replied to Laban, saying, “I did not tell you that we were planning to leave, because I was afraid. I thought that [if I told you], you would forcefully take your daughters away from me.
Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
32 But if you find anyone here who has your wooden idols, we will execute that person. While our relatives are watching, search for yourself to see if there is anything that belongs to you that is here with me. If you find anything, you can take it!” When Jacob said that, he did not know that Rachel had stolen the wooden idols.
Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
33 Laban went into Jacob’s tent, and then into Leah’s tent, and then into the tents of the two female slaves and searched for the idols, but he did not find them. After he left their tents, he entered Rachel’s tent.
Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
34 But Rachel had previously taken the idols and put them in the saddle of a camel, and she was sitting on the saddle. So when Laban searched all over for them inside Rachel’s tent, he did not find them.
Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
35 Rachel said to her father, “Do not be angry with me, sir, but I cannot get up in your presence [to show respect for you], because I am having my monthly menstrual period. [EUP]” So when Laban searched some more, he did not find the [wooden] idols.
Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
36 Then Jacob became angry. He rebuked Laban, saying, “What crime did I commit? For what sin that I committed have you pursued me?
Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
37 Now you have searched through all my possessions, and what did you find from all these possessions that belongs to you? Put it here in front of my relatives and your relatives, so that they can decide who is right, you or me!
Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
38 I was with you for 20 years. In all that time, your sheep and goats have (not miscarried/always given birth to animals safely). I have not [killed and] eaten any rams from your flocks.
“Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
39 When one of your animals was attacked and mauled/killed by a wild animal, I did not bring it to you. I replaced the dead animal with a living one of my own animals. Whenever one of your animals was stolen, during the day or during the night, you demanded that I replace it with one of my own animals.
Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
40 I suffered from the heat during the day and from the cold at night. I was often not even able to sleep [PRS]!
Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
41 I lived in your household for 20 years. I worked for you for 14 years to buy your two daughters, and for six more years to buy some of your sheep and goats. During that time, you changed and reduced my wages many times [HYP].
Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
42 If God, the one whom my grandfather Abraham worshiped and before whom my father Isaac trembled in fear, had not been with me and helped me, you would have sent me away (with nothing in my hands/owning nothing)! But God saw how much I was suffering and how hard I was working, so last night he told you that what you have done to me was wrong.”
Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
43 Laban replied, “These two women are my daughters, and their children are my grandchildren, and the animals are my animals. Everything you see here is mine [HYP]! But what can I do today to keep my daughters or the children they have given birth to [RHQ]?
Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
44 I cannot do anything in order to keep them, so hey, we should make a peace agreement, you and I, and do something that will remind us about our agreement.”
Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
45 So Jacob took a [large] stone and set it on its end.
Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
46 Then Jacob said to his relatives, “You also gather some stones.” So they gathered some rocks and put them in a heap, and they ate some food there near the heap.
Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
47 Laban gave the heap the Aramaic name Jegar-Sahadutha, [which means ‘rock-pile to remind us’, ] but Jacob gave the rock-pile the Hebrew name Galeed, [which has the same meaning].
Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
48 Laban said to Jacob, “This pile of rocks we have put here today will help us to remember our agreement.” That is why Jacob called it Galeed.
Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
49 They also named the place Mizpah, [which sounds like the Hebrew word that means ‘watchtower’, ] because Laban said, “We will ask Yahweh to watch you and me while we are separated from each other, [so that we do not try to harm each other].
Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
50 If you mistreat my daughters, or if you take other women to be your wives, even if no one tells me about it, don’t forget that God sees what you and I are doing!”
Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
51 Laban also said to Jacob, “You see this large stone and this pile of rocks that we have set up to be between us.
Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
52 Both this pile of rocks and this large stone will remind us, that I will not go past these rocks to harm you, and you will not go past these rocks to harm me.
Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
53 We will ask the God whom [your grandfather] Abraham and [his father] Nahor worshiped to punish [MTY] either one of us, [if we harm the other one].” So Jacob solemnly promised to do what they said in their peace agreement. And he asked God, the one before whom his father Isaac trembled, to listen to what they promised.
Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
54 He offered a sacrifice to God there in the hilly area, and he invited his relatives to eat with him. After they had eaten, they slept there that night.
Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
55 The next morning Laban kissed his grandchildren and his daughters [goodbye] and asked God to bless them. Then he [and his men] left them and returned home.
Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.

< Genesis 31 >