< Genesis 3 >

1 The snake was more cunning than all the other wild animals that Yahweh God had made. [One day Satan gave to] the snake [the ability to talk to the woman]. The snake said to her, “Did God really say to you, ‘Do not eat the fruit from any of the trees in the park/garden’?”
To, maciji dai ya fi kowane a cikin namun jejin da Ubangiji Allah ya yi wayo. Ya ce wa macen, “Tabbatacce ne Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga kowane itace a lambu’?”
2 The woman replied, “[What God said was], ‘Do not eat the fruit from the tree that is in the middle of the park/garden or touch it. If you do that, you will die. But you can eat fruit from any of the other trees.’”
Macen ta ce wa macijin, “Za mu iya ci daga’ya’ya itatuwa a lambun,
3
amma Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga’ya’yan itacen da yake tsakiyar lambu, kada kuma ku taɓa shi, in ba haka ba kuwa za ku mutu.’”
4 The snake said to the woman, “No, you will certainly not die. God said that
Maciji ya ce wa macen, “Tabbatacce ba za ku mutu ba.
5 [only] because he knows that when you eat fruit from that tree, [you will understand new things. It will be as though] your eyes are opened [MET], and you will know what is good [to do] and what is evil [to do], just as God does.”
Gama Allah ya san cewa sa’ad da kuka ci daga itacen idanunku za su buɗe, za ku kuma zama kamar Allah, ku san abin da yake mai kyau da abin da yake mugu.”
6 The woman saw that the fruit on that tree was good to eat, and it was very beautiful, and she desired it because [she thought] it would make her wise. So she picked some of the fruit and ate it. Then she gave some to her husband, and he ate it.
Sa’ad da macen ta ga’ya’yan itacen suna da kyau don abinci, abin sha’awa ga ido, abin marmari kuma don samun hikima, sai ta tsinka ta ci, ta kuma ba da waɗansu wa mijinta wanda yake tare da ita, shi ma ya ci.
7 Immediately [it was as though] their eyes were opened, and they realized that they were naked, so they were ashamed. So they [picked] some fig leaves and fastened them together to make clothes for themselves.
Sa’an nan idanun dukansu biyu suka buɗe, suka kuma gane tsirara suke; saboda haka suka ɗinɗinka ganyayen ɓaure suka yi wa kansu sutura.
8 [Late that afternoon], when a cool breeze was blowing, they heard the sound/footsteps of Yahweh as he was walking in the park/garden. So the man and his wife hid themselves among the bushes in the park/garden, [so that Yahweh God would not see them].
Da mutumin da matarsa suka ji motsin Ubangiji Allah yana takawa a lambun a sanyin yini, sai suka ɓuya daga Ubangiji Allah a cikin itatuwan lambu.
9 But Yahweh God called to the man, saying to him, “Why are you [trying to hide from me]?”
Amma Ubangiji Allah ya kira mutumin ya ce, “Ina kake?”
10 The man replied, “I heard the sound of your [footsteps/walking] in the garden, and I was naked, so I was afraid and I hid myself.”
Ya ce, “Na ji ka a cikin lambu, na kuwa ji tsoro gama ina tsirara, saboda haka na ɓuya.”
11 God said, “How did you find out you were naked [RHQ]? It must be because you ate some of the fruit [from the tree] that I told you, ‘Do not eat its fruit.’” [RHQ]
Sai ya ce, “Wa ya faɗa maka cewa kana tsirara? Ko dai ka ci daga itacen da na umarce ka kada ka ci ne?”
12 The man said, “You gave me this woman to be with me. She is the one who gave me some of the fruit from that tree, and so I ate it.”
Mutumin ya ce, “Macen da ka sa a nan tare da ni, ita ta ba ni waɗansu’ya’ya daga itacen, na kuwa ci.”
13 Then Yahweh God said to the woman, “Why did you do such a thing?” The woman replied, “I ate some of the fruit because the snake deceived me.”
Sai Ubangiji Allah ya ce wa matar, “Me ke nan kika yi?” Matar ta ce, “Macijin ne ya ruɗe ni, na kuwa ci.”
14 Then Yahweh God said to the snake, “Because you did this, of all the livestock and the wild animals, I will curse/punish you alone. As a result, you [and all other snakes] will scurry across the ground on your bellies, and so what you eat will have dirt [on it] as long as you live.
Saboda haka Ubangiji Allah ya ce wa macijin, “Saboda ka yi haka, “Na la’anta ka cikin dukan dabbobi da kuma cikin dukan namun jeji! Daga yanzu rubda ciki za ka yi tafiya turɓaya kuma za ka ci dukan kwanakin rayuwarka.
15 And I will cause you and the woman to act in a hostile way toward each other, and I will cause your brood and her descendants to act hostilely toward each other. You will strike at the heel [of one descendant] of hers, but he will strike your head.”
Zan kuma sa ƙiyayya tsakaninka da macen, tsakanin zuriyarka da zuriyarta. Zai ragargaje kanka, kai kuma za ka sari ɗiɗɗigensa.”
16 Then Yahweh said to the woman, “You will have great pain when you give birth to children; you will suffer great pain as your children are being born [DOU]. You will greatly desire your husband [to show affection for you], but he will rule over you.”
Sa’an nan ya ce wa macen, “Zan tsananta naƙudarki ainun, da azaba kuma za ki haifi’ya’ya. Za ki riƙa yin marmarin mijinki zai kuwa yi mulki a kanki.”
17 Then Yahweh said to the man, “You heeded what your wife said, and you ate some of the fruit [of the tree] concerning which I commanded you saying, ‘Do not eat it.’ So I will make it difficult [to grow things in] the ground because of what you did. You will have to work hard as long as you live to produce things from the ground to eat.
Ga Adamu kuwa ya ce, “Saboda ka saurari matarka, ka kuma ci daga itacen da na ce, ‘Kada ka ci,’ “Za a la’anta ƙasa saboda kai. Da wahala za ka ci daga cikinta dukan kwanakin rayuwarka.
18 Thornbushes and thistle plants and other weeds will grow [and prevent what you have planted from growing]. And for food, you will have to eat things that just grow in your fields.
Za tă ba ka ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za ka kuwa ci ganyayen gona.
19 [All your life] you will sweat as you work hard to produce food to eat. Then you will die [EUP], and your [body will be buried] in the ground. [I made] you from soil, so when you [die and are buried your body will decay] and become soil again.”
Da zuffan goshinka za ka ci abincinka har ka koma ga ƙasa, da yake daga cikinta aka yi ka. Gama kai turɓaya ne, kuma ga turɓaya za ka koma.”
20 [The man, whose name was] Adam, named his wife Eve, [which means ‘living’], because she became the ancestor of all living people.
Mutumin ya sa wa matarsa suna, Hawwa’u, gama za tă zama mahaifiyar masu rai duka.
21 Then Yahweh God [killed some animals and] made clothes from their skins for Adam and his wife.
Ubangiji Allah ya yi tufafin fata domin Adamu da Hawwa’u, ya kuma yi musu sutura.
22 Then Yahweh said, “Look! Those two have become like us because they know what is good [to do] and what is evil [to do]. So now, it will not be good if they reach out and pick and eat [some of the fruit from] the tree [which enables people who eat it] to live [forever]!”
Ubangiji Allah ya kuma ce, “To, fa, mutum ya zama kamar ɗaya daga cikinmu, ya san abin da yake mai kyau da abin da yake mugu. Kada a yarda yă miƙa hannunsa yă ɗiba daga itacen rai yă ci, yă kuma rayu har abada.”
23 So Yahweh God expelled the man and his wife from the garden of Eden. Yahweh God had created Adam from the ground, but now he forced him to till that ground [so that he could grow food to eat].
Saboda haka Ubangiji Allah ya kore shi daga Lambun Eden domin yă nome ƙasa wadda aka yi shi.
24 After Yahweh expelled them, on the east side of the garden he placed (cherubim/creatures with wings) and [an angel holding] a flaming sword which flashed back and forth. He did that in order to block the entrance to the garden, so that people could not go back to the tree that enables people [who eat its fruit] to live [forever].
Bayan da ya kori mutumin, sai ya sa kerubobi da takobi mai harshen wuta yana jujjuyawa baya da gaba a gabashin Lambun Eden don yă tsare hanya zuwa itacen rai.

< Genesis 3 >