< Genesis 21 >

1 Yahweh was very kind to Sarah, just as he said he would be. He did for Sarah exactly what he promised to do.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 She became pregnant and gave birth to a son for Abraham when he was very old, at the time God promised it would happen.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 Abraham gave the name ‘Isaac’ (which means ‘he laughs’) to the son Sarah gave birth to.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 Abraham circumcised his son Isaac when his son was eight days old, just as God commanded him to do.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 Abraham was 100 years old when his son Isaac was born.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 And Sarah said, “[Although I was sad before because I did not have any children], God has now enabled me to laugh, and everyone who hears about what God has done for me will laugh with me.”
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 Then she also said, “No one would have said to Abraham that some day Sarah would nurse a child, but I have given birth to a son when Abraham is very old.”
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 The baby grew and was weaned [when he was about three years old]. On that day, Abraham prepared a large feast to celebrate.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 ([One day/During the feast)] Sarah noticed that Hagar’s son Ishmael was (making fun of/playing with) Isaac.
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 So she said to Abraham, “Get rid of that slave woman from Egypt and her son! I do not want the son of that slave woman to be alone (OR, to be an heir along with) my son, Isaac!”
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 Abraham was very distressed about the matter, because he was concerned about his son [Ishmael].
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 But God said to Abraham, “Do not be distressed about your son, Ishmael, and about your maidservant, Hagar. Do everything that Sarah tells you to do. Listen to her, because Isaac is the one who will be considered the ancestor of the descendants I promised to give you.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 But I will also cause the son of your maidservant to be the ancestor of the people of a great nation [MTY], because he is also your son.”
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 So Abraham got up early the next morning. He got some food ready, put water in a container, and gave them to Hagar. He put them [in a bag] on her shoulder and sent them away. They wandered in the desert near Beersheba [town].
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 After they had drunk all the water in the container, she put her son under one of the bushes there.
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 Then she went and sat nearby, about (as far as someone can shoot an arrow/100 meters away), because she thought, “I cannot endure seeing my son die!” As she sat there, she began to cry [loudly] [MTY].
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 [The boy was crying too.] And God heard the boy crying. So he caused one of his angels to call out from heaven to Hagar, saying, “Hagar, are you worried about something? Do not be afraid, because God has heard the boy crying there.
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Help your son up, and hold his hand as you leave, because I will cause his descendants to become a great nation.”
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 Then God showed her a well of water. So she went to the well and filled the container with water, and gave the boy a drink.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 God helped the boy as he grew up. He lived in the desert and became a good (archer/man who hunts with bow and arrows).
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 He lived in Paran Desert. While e was there, Hagar got a wife for him from Egypt.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 At that time, [King] Abimelech and Phicol, the commander of his army, said to Abraham, “It is clear that God helps you with everything that you do.
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 So now (solemnly promise/swear) to me here, as God is listening, that you will (not deceive/act fairly to) me and my children and my descendants, in return for my being kind to you. Be kind to me and to all the people here in the country where you are now living.”
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 So Abraham promised to do that.
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 [Then] Abraham complained to Abimelech about one of Abraham’s wells that Abimelech’s servants had seized.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 But Abimelech said, “I do not know who has done that. You did not tell me previously, and I did not hear about it until today.”
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 So Abraham brought some sheep and gave them to Abimelech, and the two of them made a (treaty/peace agreement).
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 Abraham separated seven female lambs from his flock.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 Abimelech asked Abraham, “What are these seven female lambs that you have separated from the rest of your flock?”
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 Abraham replied, “I want you truly to accept these female lambs from me [SYN], so that it may be a (public witness/proof) that this well belongs to me because I dug it.”
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 So Abimelech accepted the animals, and as a result they called that place Beersheba, [which means ‘Friendship Agreement Well’, ] because there the two of them made that agreement.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 After they made the agreement at Beersheba, Abimelech and his army commander, Phicol, left, and returned to the land of the Philistine people-group.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 Abraham planted a (tamarisk tree/kind of tree called esel) there, and he worshiped the eternal God there.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 Abraham lived in the land of the Philistine people-group for a long time.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.

< Genesis 21 >