< Ezra 8 >

1 This is a list of the names of the leaders of the clans who came with me up [to Jerusalem] from Babylonia when Artaxerxes was the king [of Persia]:
Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
2 Gershom, from the clan descended from [Aaron’s grandson] Phinehas Daniel, from the clan descended from [Aaron’s son] Ithamar Hattush, the son of Shecaniah, from the clan descended from King David
Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
3 Zechariah and 150 [other] men from the clan descended from Parosh
ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
4 Eliehoenai the son of Zerahiah and 200 other men from the clan descended from Pahath-Moab
daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
5 Shecaniah the son of Jahaziel and 300 other men from the clan descended from Zattu
daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
6 Ebed the son of Jonathan and 50 other men from the clan descended from Adin
daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
7 Jeshaiah the son of Athaliah and 70 other men from the clan descended from Elam
daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
8 Zebadiah the son of Michael and 80 other men from the clan descended from Shephatiah
daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
9 Obadiah the son of Jehiel and 218 other men from the clan descended from Joab
daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
10 Shelomith the son of Josiphiah and 160 other men from the clan descended from Bani
daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
11 Zechariah the son of Bebai and 28 other men from the clan descended from [another man whose name was] Bebai
daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
12 Johanan the son of Hakkatan and 110 other men from the clan descended from Azgad
daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
13 Also Eliphelet, Jeuel, and Shemaiah, who returned [here] later with 60 men from the clan descended from Adonikam
zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
14 And Uthai and Zaccur and 70 other men from the clan descended from Bigvai.
daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
15 I gathered all of them together at the canal that goes [from Babylon] to Ahava [town]. We set up our tents there and stayed there for three days. [During that time] I checked the lists of names and found out that there were priests [going with us], but no [other] descendants of Levi [who could help them in the temple].
Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
16 So I summoned Eliezer, Ariel, Shemaiah, two men whose names were Elnathan, and Jarib, Nathan, Zechariah, and Meshullam, who were all leaders [of the people]. I also summoned Joiarib and another Elnathan, who were wise.
Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
17 I sent them all to Iddo, the leader of the descendants of Levi, who was living in Casiphia [town], to request that he and his relatives and other men who had worked in the temple send to us some men who would [go/come with us to] work in God’s new temple [in Jerusalem].
Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
18 Because God was kind to us, they brought to us a man named Sherebiah and 18 of his sons and other relatives. Sherebiah was a very wise man, a descendant of Mahli, [who was a grandson] of Levi.
Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
19 They also sent to us Hashabiah, along with Jeshaiah, descendants of [Levi’s son] Merari, and 20 of their relatives.
Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
20 They also sent 220 other men to work in the temple. Those men’s ancestors had been appointed by King David to assist the descendants of Levi [who helped the priests in the temple]. I listed/wrote the names of all those men.
Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
21 There alongside the Ahava Canal, I told them that we all would (fast/abstain from eating food) and pray. I also told them that we should humble ourselves in the presence of our God. We prayed that God would protect us while we traveled, and also protect our children and our possessions/belongings.
A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
22 Previously we had told the king that our God takes care of all those who truly trust in him, but that he becomes very angry with those who refuse to obey him. So I would have been ashamed if I had asked the king to send soldiers and men riding on horses to protect us from our enemies while we were traveling along the road.
Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
23 So we (fasted/abstained from eating food) and requested God to protect us, and he (answered our prayers/did what we requested.)
Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
24 I chose twelve of the leaders of the priests, Sherebiah and Hashabiah and ten of their relatives.
Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
25 I appointed them to supervise carrying to Jerusalem the gifts of silver and gold and the other valuable items that the king and his advisors and other officials, and the Israeli people [who were living in Babylonia], had contributed for the temple of our God.
Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
26 As I gave these various items to those priests, I weighed each of the items. This was the total: 25 tons of silver, 100 items made from silver that altogether weighed 7,500 pounds, (7,500 pounds/3,400 kg.) of gold,
Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
27 20 gold bowls that altogether weighed (19 pounds/8.6 kg.), and two items made of polished bronze that were as valuable as ones made of gold.
kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
28 I said to those priests, “You belong to Yahweh, the God whom our ancestors (worshiped/also belonged to), and these valuable things also belong to him. The people themselves gave these things to be offerings to Yahweh (voluntarily/because they wanted to).
Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
29 So guard them carefully, and [when we arrive] in Jerusalem, weigh them in the presence of the priests, the descendants of Levi [who will help the priests], and the other Israeli leaders there. They will then put them in the storerooms in the new temple.”
Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
30 So the priests and [other] descendants of Levi took from me all the gifts of silver and gold and the other valuable items, in order to carry them to the temple in Jerusalem.
Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
31 On April 19, we left the Ahava Canal and started to travel to Jerusalem. Our God took care of us, and while we traveled, he prevented our enemies and bandits from (ambushing us/suddenly attacking us).
A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
32 After we arrived in Jerusalem, we rested for three days.
Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
33 Then on the fourth/next day we went to the temple. There the silver and gold and the other items were weighed and given to the priest Meremoth, the son of Uriah. Eleazar the son of Phinehas and two descendants of Levi, Jozabad the son of Jeshua and Noadiah the son of Binnui, were with him.
A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
34 They counted everything, and wrote down how much they weighed, and wrote [a description of] each item.
Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
35 We who had returned from Babylonia offered to God sacrifices on the altar. We offered twelve bulls for all us Israeli people. We also offered 96 rams and 27 lambs. We also sacrificed twelve goats [to atone] for the sins that all the people had committed. These were all completely burned on the altar.
Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
36 Some of us who returned [from Babylonia] took to the governors and other officials of the province west of the [Euphrates] River the letter that the king had given to us. [After they read the letter, ] they did all [that they were able to do] for us Israeli people and for the temple of God.
Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.

< Ezra 8 >