< Ezekiel 38 >

1 Yahweh gave me another message. He said to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, turn and face Magog, the country where Gog [is the king]. He is [also] the ruler of [the nations of] Meshech and Tubal. Prophesy about [the terrible things that will happen to] him,
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
3 and say, ‘This is what Yahweh the Lord says: Gog, you who rule Meshech and Tubal, I am opposed to you.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
4 [It will be as though] I will turn you around and put hooks in your jaws and bring you [to Israel]—you and all of your army, [including your] horses and men carrying weapons who ride the horses, and many other soldiers carrying large shields and small shields, all of them carrying swords.
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
5 [Armies from] Persia, Ethiopia, and Put/Libya will also come, all of them with shields and helmets.
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
6 An army from Gomer [north of Israel] will come, and an army from Togarmah far north [of Israel] will come. Armies of many nations will accompany you.’
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
7 [Tell Gog, ] ‘Get ready and be prepared to be the commander of all those groups of soldiers.
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
8 At some future time, I will command you to lead those armies to attack [Israel], a country whose [buildings] have been rebuilt after [they were destroyed in] wars. Their people will have been brought back from many nations [to live again] on the hills of Israel, which had been deserted for a long time. They had been brought back from [other] nations and will be living peacefully.
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
9 You and all those armies from many nations will go up to Israel, advancing like [SIM] a big storm. Your army will be like a huge cloud that covers the land.
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
10 But this is what [I], Yahweh the Lord, say: On that day, you will have an idea about [DOU] doing an evil thing.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
11 You will say [to yourself], “My [army] will invade a country where the villages do not have walls around them. We will attack people who are peaceful and do not suspect/think [that they will be attacked]. Their towns and villages do not have walls with gates and bars.
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
12 So [it will be easy for] us to attack the people who are living again in those towns that were previously destroyed. They are people who have been gathered from many countries [where they had lived for many years], people who now live safely in their land with all their livestock and other possessions. They are living in the country that is in the middle of the most important countries (OR, [that they think is] [IRO] the most important country) in the world. Our soldiers will take away [DOU] all their valuable possessions.”
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
13 [Then people of] Sheba and Dedan and the merchants of Tarshish and nearby villages will come and say to you, “Are you gathering all your soldiers in order to [attack Israel and] take away all their silver and gold? [Do you plan] to take away their livestock and all their other valuable possessions [DOU]?”’
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
14 Therefore, you human, prophesy about Gog and say to him, ‘This is what Yahweh the Lord says: At that time, when my people of Israel are living safely, you will certainly think about that.
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
15 So you will come from your place far north [of Israel], with the armies of many [other] nations, all riding horses, a huge army.
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
16 You will march toward my Israeli people, and [your soldiers] will cover the land like a huge cloud. Gog, I will bring your army to attack the country that belongs to me, but [what I do] for you will show the people of other nations that I am holy.
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
17 This is what [I], Yahweh the Lord, say to Gog: In past years, when I gave messages to my servants, the prophets [in Israel], there were messages [RHQ] about you. At that time, they prophesied for [many] years that I would bring your [armies] to attack my people.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
18 [So] this is what I, Yahweh the Lord, say will happen: When your [army] attacks Israel, I will be very angry with you.
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
19 I will be very furious, and to show that I am angry, there will be a great earthquake in Israel, [where your armies will be].
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
20 The fish in the sea, the birds, the wild animals, and the animals/creatures that crawl on the ground, and all the people on the earth will tremble because of what I [am doing]. Mountains will fall down, cliffs will crumble, and walls everywhere will fall to the ground.
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
21 Gog, on all the mountains in the country that belongs to me I will cause your soldiers to fight against each other with their swords.
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
22 I will punish [MTY] you [and your soldiers] with plagues and murders [MTY]. And I will send down [from the sky], on you and your troops that have come from many nations, huge amounts of rain and hail and burning sulfur.
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
23 By doing that, I will cause [the people of] many nations to know that I am very great and holy, and they will know that I, Yahweh, [have the power to do the things that I say that I will do].’”
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’

< Ezekiel 38 >