< Ezekiel 34 >

1 Yahweh gave me another message. He said,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, prophesy about [leaders] of Israel. [They should be taking care of my people like] [MET] shepherds [take care of their sheep]. Say to them, ‘This is what Yahweh the Lord says: Terrible things will happen to you leaders [MET] of Israel who only take care of yourselves! You should certainly [RHQ] take care of [your people like] [MET] a shepherd takes care of his flock of sheep!
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
3 [It is as though] you eat the curds, you slaughter the very good animals and wear clothes made from their wool. But you do not take care of the flock.
Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
4 You have not enabled those who are weak to become strong. You have not healed those who were sick. You have not bandaged those who were wounded/injured. You have not brought back those who went astray. You have not searched for those who became lost. You have ruled your people harshly and cruelly.
Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
5 So they were scattered, because you did not [take care of them like] [MET] a shepherd [takes care of his sheep]. And when they were scattered, [it was as though] wild animals attacked and [killed them and ate] their flesh.
Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
6 My people wandered like sheep all over the high hills and mountains. They were scattered all over the earth, and no one searched for them [DOU].
Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
7 Therefore, you [who should be acting like] shepherds, listen to what I, Yahweh the Lord say:
“‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
8 As surely as I am alive, my people [are like a flock of sheep that has] no shepherd, and as a result [it is as though] wild animals have attacked my people and eaten them. You did not search for them; instead, you only wanted to provide food for yourselves.
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
9 Therefore, you [who should be like] [MET] shepherds, listen to what I, Yahweh say:
saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
10 I am opposed to [you leaders who should be like] [MET] shepherds for my people. I will remove you from taking care of my people, with the result that you will no longer feed yourselves [instead of feeding them]. I will rescue my people from you, with the result that you will longer be able to [butcher them and] eat them.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
11 This is what I, Yahweh the Lord, say to you leaders: I myself will search for my sheep and take care of them.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
12 Like a shepherd finds his scattered sheep, I will rescue my people from all the places to which they have been scattered, at a time when things were very gloomy and they experienced disasters.
Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
13 I will bring them back from many countries and gather them together again in their own land. [Because my people are like sheep] [MET], [it is as though] I will enable them to find good pastureland on the hills of Israel, and in the ravines, and in the villages of Israel.
Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
14 [It is as though] I will allow them to graze in good pastures on the mountaintops. They will lie down in good (grazing areas/grassy fields) there [DOU].
Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
15 I myself will take care of my people and enable them to lie down and rest.
Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 I will search for those who are lost and bring back the ones who have strayed away. I will bandage those who have been injured and strengthen those who are weak. But I will get rid of those who are fat and powerful. I will act fairly toward [the people who are like] [MET] my sheep. That is what I, Yahweh, promise.
Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
17 And as for you who are like [MET] my sheep, this is what I, Yahweh the Lord, say: I will judge between each of you; and I will separate [those that are peaceful like] sheep from [those that are always trying to dominate others like] goats.
“‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
18 It is bad that [RHQ] some of you keep the best pastures for yourselves. It is even worse that [RHQ] you trample the good grass with your feet. You yourselves drink the clear water [RHQ]. But with your feet you cause the other water to become muddy [RHQ].
Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
19 [It is as though] you [RHQ] are forcing my flock to eat the grass that you have trampled and to drink the water that you have caused to become muddy!
Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
20 Therefore, this is what I, Yahweh the Lord, say to you: I myself will judge between [those of you who are like] [MET] the fat sheep and [those of you who are like] the thin sheep.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
21 [who are like] strong sheep, [it is as though] with your shoulders and buttocks you have shoved away [those who are like] thin sheep, and you have butted them with your horns, until you have chased them all away [from the good pastureland].
Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
22 But I will rescue my people, and they no longer will be (harassed/treated cruelly). I will judge between one person and another.
zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
23 And I will appoint one leader [MET] for them, [someone who will be like] King David, who served me [very well]. That leader will take care of them and be like their shepherd.
Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
24 I, Yahweh, will be their God, and [the one who is like] [MET] King David will be their king. [That will surely happen because] I, Yahweh, have said it.
Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
25 I will make a peace agreement with the people of Israel. In this agreement I will promise to get rid of all the wild animals in Israel, in order that my people may live safely, even in the desert and in the forests.
“‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
26 I will bless them, and I will bless the places close to my sacred hill. I will bless them by sending them rain showers at the right season; they will be showers to bless them.
Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
27 The fruit trees will produce fruit and the ground will produce crops. And my people will live safely in their land. When I rescue them from people who caused them to be slaves [MET, DOU], they will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
28 [Soldiers from] other nations will no longer take away their valuable possessions, and wild animals will no longer attack them. They will live safely, and no one will cause them to be afraid.
Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
29 I will cause their land to be famous/well-known for its good crops. There will no longer be famines in the land, and people in other nations will no longer ridicule them.
Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
30 Then they will know that I, Yahweh their God, am helping them, and they will know that they, the Israeli people, are my people.
Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
31 [It will be as though] [MET] my people are my sheep whom I will take care of, and I will be their God. That is what I, Yahweh the Lord, declare.’”
Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 34 >