< Ezekiel 24 >

1 Almost nine [after we had been taken to Babylonia], on the tenth day of the tenth month [of that year], Yahweh gave me this message:
A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, write down what day of the month this is. On this [the army of] King of Babylon has surrounded Jerusalem.
“Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
3 Tell those rebellious Israeli people [MTY] [in Babylon] a parable. Say this to them: This is what Yahweh the Lord says: ‘Pour water into the [cooking] pot and put the pot [the fire].
Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
4 Put into the pot some pieces of [from one of your best sheep]: Put in the leg and shoulder, [which are] the best pieces. [Then] fill [the rest of] the pot with the best bones.
Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
5 Pile wood on the fire, and cook the bones and the meat in the boiling water.’
ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
6 [Do that] because this is what Yahweh the Lord says: ‘Terrible things will happen [Jerusalem]; it is city that is full of murderers [MTY], [a city that is like] [MET] a scorched pot whose black residue inside cannot be removed. Take the pieces [of meat] out of the pot, but do not choose which pieces to take out.
“‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
7 The blood of the people who were murdered in Jerusalem is still there; they were murdered on the bare rocks, not on the soil, where their blood could be covered.
“‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
8 But I am the one who caused the blood of those who were murdered [MTY] to be smeared on the bare rock, where their blood could not be covered; I did that in order [I could see it and] then be angry and get revenge.’
Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
9 Therefore, this is what [I], Yahweh the Lord say: ‘Terrible things will happen to that city that is full of murderers [MTY]! [It will be as though] I also will pile high [the wood in the fire].
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
10 [So], heap on the wood and light the fire! Cook the meat well, and mix some spices with it; cook it until the bones are charred.
Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
11 Then set the empty pot on the [of the fire] until the pot becomes [very] hot and the copper glows, with the result that the impurities and the rust will be burned up.
Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
12 [It is as though] I tried to get rid of that rust, but I was not able to do it, [not even] by putting that pot in a fire.
Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
13 The [in the pot represents] your immoral behavior. I tried to cleanse you from your wicked behavior, but you did not allow me to do that. So you will not be [from the guilt of your sin] [I have punished you and] I am no longer angry.
“‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
14 I, Yahweh, have said [that I will surely punish you]. [And it is time] for me to do that. I will not change my mind; I will not refrain from punishing you, and I will not pity you. I will judge you [and punish you] as you deserve to be punished for your sinful behavior. [That will surely happen because] I, Yahweh the Lord, have said it.”’”
“‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 [One day] Yahweh gave me this message:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 “You human, I am going to suddenly take from [your wife], whom you love very much. [when she dies], do [show that you are] sad or lament or cry.
“Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
17 Groan quietly; do not cry [openly] for her. [Keep] your turban wrapped around your head, [instead of being barefoot, keep] your sandals on your feet. Do not cover the lower part of your [to show that you are sad]. And do not eat the kind of food that people who are mourning usually eat.”
Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
18 [one morning] I talked to the [as usual], and that evening my wife [suddenly] died. The next morning I did what [Yahweh] had told me to do.
Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
19 Then the people asked me, “What do the things that you are doing signify to us?”
Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
20 So I said to them, “[This is what] Yahweh told me:
Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
21 ‘Tell the Israeli people [MTY] that I am about to destroy the temple, [the building] that you are very proud of, the building that you delight to look at. Your children whom you [in Jerusalem when you were forced to come to Babylon] will be killed [their enemies’] swords.
faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
22 [When that happens], you will do like I have done: You will not cover the lower part of your faces, or eat the kinds of food that people who are mourning usually eat.
Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
23 [You will keep] your turbans wrapped around your heads and [keep] your sandals on your feet. You will not mourn or cry, but your bodies will become very thin and slowly die because of your sins. And you will groan to each other.
Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
24 Ezekiel will be a warning to you, and you must do what he has done. When that happens, you will know that I, Yahweh the [have the power to do what I say that I will do].’”
Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
25 [Then Yahweh said to me], “You human, [soon] I will destroy their sacred temple, which they rejoice about and which they respect and delight to look at, and [I will get rid of] their sons and daughters also.
“Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
26 On that day, someone will escape [from Jerusalem] and come and tell you what has happened [there].
a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
27 When that happens, you will be able to speak again [MTY] [without constraint]. You two will talk together [DOU]. You will be a warning to the people; and they will know that I, Yahweh the Lord, [have the power to do what I say that I will do].”
A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 24 >