< Ezekiel 22 >

1 Yahweh gave me another message. He said,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, are you ready to condemn the people of Jerusalem? It is [RHQ] a city full of murderers [MTY]. Remind them of all the detestable things that they have done.
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 [Then] say, ‘This is what Yahweh the Lord says: By your murdering people and by (defiling yourselves/making yourselves unacceptable to God) by making idols, you people of this city [APO] have brought to yourselves the time when you [will be destroyed].
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 You have become guilty by doing both of those things [DOU]. You have brought to an end your time [to remain alive] [DOU]. Therefore I will cause you to become a group whom the [people of other] nations will scorn; they will all laugh at you [DOU].
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 People in countries that are near you and people who live far from you will make fun of you, because your city is full of lawless people and full of confusion.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Think about how each of your Israeli kings have used their power to cause people to be murdered [MTY].
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 Your people do not respect/honor their parents; they have oppressed foreigners; they mistreat orphans and widows.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 You despise my sacred places and (dishonor/do not respect) the Sabbath days.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 Among you are men who tell lies in order to cause others to be executed [MTY]. There are those who [food offered to idols] at the hilltop [shrines], and they perform disgusting sexual acts.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 There are men who have sex with their father’s wives [EUP], and men who have sex with women during their monthly menstrual periods.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 There are men who have sex with someone else’s wife. Some men have sex with their daughters-in-law or with their sisters or half-sisters.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 There are among you men who accept bribes in order to cause someone to be executed [MTY]. You charge high interest when you lend people money. You become rich by forcing people to give you money. [the worst thing is that] you have forgotten me, Yahweh the Lord.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 So I will shake my fists at you to show that I am angry with you because of your stealing money from people and murdering [MTY] people who live among you.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 When I [punishing] you, you will no longer [RHQ] be courageous/brave [DOU]. I, Yahweh, have said [what I will do to you], and I will do it.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 I will cause you to be scattered among many nations [DOU], and I will cause you to stop your sinful behavior.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 When [the people of other] nations see that you have been humiliated, you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].’”
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 Yahweh [also] said to me,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “You human, your Israeli people [MTY] have [useless] to me. They are [like] [MET] dross/slag to me. They are like [SIM] [worthless] copper, tin, iron, and lead that remains after silver is melted in [very hot] furnace.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Therefore, this is what [I], Yahweh the Lord, say: Because you have all become [like] dross/slag, I will gather you in Jerusalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 People [ore containing] silver, copper, iron, lead, and tin in a [very hot] furnace and melt them in a blazing [to burn up the impurities]. Similarly [SIM], I will gather you [inside Jerusalem], and because I am very angry with you, [what I will do will be as though] I am melting you.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 [It will be as though] I will blow on you with a hot breath that shows that I am very angry, [it will be as though] you will be melted,
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 as though you will be melted like [SIM] silver is melted in a furnace, and then you will know that I, Yahweh, have poured out my punishment [MTY] on you.”
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 Yahweh gave me another message. He said,
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 “You human, say to the Israeli people, ‘[Yahweh] is angry with you, there has been no rain or showers in your country.’
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Your leaders are like [SIM] lions that tear apart the animals that they have killed. Your leaders destroy their people. They steal treasures and [other] valuable things from people, and they cause many women to become [by murdering their husbands].
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Their priests disobey my laws and disrespect my sacred things by saying that there is no difference between things that are sacred and those that are not sacred, and by ignoring my laws about honoring the Sabbath days. As a result, they no [longer] honor me.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Their officials are like [SIM] wolves that tear apart the animals that they have killed: They murder people [DOU] in order to get their money.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Their prophets, by falsely saying they have received [from God], and by giving false messages, try to (cover up [MET]/say that it is all right to commit) those sins. They say, ‘This is what Yahweh the Lord says,’ when I have said nothing to them.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 The Israeli people force others to give them money, and they rob people. They oppress poor [DOU] people, and they mistreat foreigners among them by not treating them [in the courts].
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 I looked among them to find a man who would cause the people of the city to repent [MET] so that I would not need to get rid of them. But I did not find anyone.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 So because I am very angry with them, I will severely punish them [MTY] for [all] the wicked things that they have done. [That will surely happen because I], Yahweh the Lord, have said it.”
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 22 >