< Ezekiel 15 >

1 Yahweh gave me another message. [He said],
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, the wood of a grapevine is certainly not [RHQ] more useful that the branches of the trees in a forest.
“Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
3 No one [RHQ] ever takes a branch of a grapevine and makes anything [useful] from it. No one [RHQ] even makes pegs from them to hang things on.
An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
4 And after a branch of a grapevine is thrown into a fire, and the fire burns both ends and chars/scorches the branch in the middle, will it then be useful for anything?
Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
5 No; if it was not useful for anything before it was burned, it certainly cannot [made into something] useful after the fire has burned and charred it.
In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
6 Therefore, this is what [I], Yahweh the Lord, say: The wood of grapevines is useful only for fuel in a fire. Similarly, the people who live in [are useless].
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
7 I will reject [IDM] them. [It will be as though] they have escaped from a fire, but there will still be a fire that will burn them up. And when I punish [EUP] them, you [people who remain alive] will know that I, Yahweh, [have done it].
Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
8 I will cause your country to become a wasteland because your people have not been loyal [to me. That is what I], Yahweh, the Lord, say.”
Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 15 >