< Ezekiel 13 >

1 Yahweh gave me another message. [He said, ]
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, [a warning] against the prophets in Israel who are prophesying. Some of them are prophesying things that they themselves have imagined/thought. Say to them: 'Listen to what Yahweh says!
“Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 He says, “Terrible things will happen to those wicked prophets who proclaim their own ideas and have not seen [visions from me].
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
4 You Israeli people, your prophets [as useless] as [SIM] jackals/wolves [that only dig] through the [of a city].
Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
5 Those prophets have not helped you Israeli people [MTY] to repair the places where [city] walls have (been broken/crumbled). That needs to be done in order that the walls will be strong at the time when I, Yahweh, [allow your enemies] to attack you.
Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
6 The visions and prophecies of those prophets are false. They say, 'Yahweh told me this,' but I have not sent [to you to be my prophets]. But they expect that what they prophesy will truly happen!
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7 They say that they have seen visions, but those visions are false, and the things that they prophesy are lies [RHQ]. They say, 'Yahweh told me this,' but I have told them nothing!”
Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
8 Therefore, this is what I, Yahweh the Lord, say: “Because you prophets have said what is false, and because your visions are lies, I am opposed to you.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 I will strike/punish all you prophets who falsely say that you have seen visions and prophesy things that are lies. You will not have any place among my people, your names will not be listed in the records of the Israeli people, and you will never return to Israel. Then you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].”
Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
10 They deceive my people, saying “Things will go well for us,” when things will not go well. [It as though] [MET] the people have built a shaky/weak wall, and the prophets cover it with (whitewash/white paint) [to make people think that it is a very strong wall].
“‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
11 So, tell those prophets who cover the wall with whitewash that the wall will surely fall down. It will rain very hard. I will send big hailstones to fall. Very strong winds will blow against it.
saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
12 When the wall falls down, the people will certainly say to those prophets, “The white paint certainly did not [RHQ] make the wall strong!”
Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
13 So this is what I, Yahweh the Lord, say: “Because I am very angry with you, [I will send enemy armies to destroy Jerusalem. It will be as though] [MET] I will send a very strong wind and hailstones and very heavy rains to destroy you.”
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
14 [The false prophecies of your prophets are like] [MET] a wall that they have covered with whitewash, but I will break it down, and shatter it down to the ground, with the result that people can see its foundations. When the wall collapses, you also will be killed, and everyone will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
15 In that way I will show that I am very angry [the people who built] the wall and those who covered it with (whitewash/white paint). Then I will say to you, “The wall is destroyed/gone, and those prophets who put (whitewash/white paint) on it have been killed.”
Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
16 Those are the prophets who prophesied that things would go well for the people in Jerusalem, when things would not go well for them.
waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
17 So, you human, show that you are angry with [IDM] the women of Jerusalem who prophesy things that they themselves have imagined.
“To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
18 Tell them, “This is what Yahweh the Lord says: Terrible things will happen to you women who fasten magic charms on your wrists and make veils of various sizes to put on your heads in order to deceive the people. [You think that] [RHQ] you will deceive [by telling them that you know what will happen in the future], and that you will save your own lives.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
19 You dishonored [by telling lies] in order to get from my people a few handfuls of barley and a few pieces of bread. My people listen to lies; and you women who are lying to them have caused to be killed people who did not deserve to die and have (spared/allowed to remain alive) those who should not continue to live.”
Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
20 Therefore, this is what I, Yahweh the Lord, [to those women]: “I detest your magic charms by which you deceive people like [SIM] [people trap] birds. I will tear those charms off your wrists, and I will cause the people whom you have deceived to no longer be deceived by you.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
21 I will also tear off your veils and rescue my people from continuing to be deceived by you, and they will no longer be under your control. Then you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
22 You have discouraged righteous people by telling them lies when I did not [do things to] cause them to be sad. And you have encouraged wicked people to not turn away from their wicked behavior; if they had done that, they would have continued to remain alive.
Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
23 Therefore, you will no longer falsely say that you have seen visions or tell people what will happen in the future [in order to please them]. I will rescue my people from being deceived by you. And then you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].” '”
saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”

< Ezekiel 13 >