< Ezekiel 10 >

1 Then [in the vision] I saw what resembled a throne made of (sapphire/[a very valuable] blue stone). It was above the thing that resembled a dome that was above the heads of the four winged creatures.
Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
2 Yahweh said to the man wearing the linen robe, “Go between the wheels that are under the winged creatures. Pick up as many hot coals as you can, and scatter them over the city.” And while I watched, the man wearing the linen robe left.
Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
3 The four winged creatures were standing on the south side of the temple when the man wearing the linen robe entered. Then a cloud filled the inner courtyard [of the temple area].
Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
4 And the (glory/dazzling light) of Yahweh rose up from above the winged creatures and went to the entrance of the temple. The cloud filled the temple, and the courtyard was full of the (glory/dazzling light) of Yahweh.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
5 The sound made by the wings of the winged creatures could be heard as far away as the courtyard outside the temple. It [very loud], like [SIM] the voice of Almighty God when he speaks.
Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
6 When Yahweh commanded the man wearing the linen robe to take burning coals from among those winged creatures, the man went [the courtyard] and stood beside one of the wheels.
Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
7 Then one of those winged creatures reached out his hand to the fire that was there among them. He picked up some of the coals and put them in the hands of the man wearing the linen robe, and that man took them and left.
Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
8 Under the wings of the winged creatures was something that resembled a human’s hands.
(A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
9 Then [in the vision] I saw four wheels alongside the winged creatures. There was one wheel beside each of the winged creatures. The wheels shone like [SIM] very valuable stones.
Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
10 The wheels were all alike: Each had one wheel inside another wheel.
Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
11 Whenever they moved, they went straight in whatever direction one of the winged creatures faced. The wheels did not turn in another direction while the winged creatures flew.
Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
12 Their bodies, including their backs and hands and wings, were covered with eyes. The wheels were also covered with eyes.
Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
13 I heard someone call them ‘the whirling wheels’.
Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
14 Each of the winged creatures had four faces. One face was like the face of a bull, one face was like the face of a human, one face was like the face of a lion, and one face was like the face of an eagle.
Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
15 Then the winged creatures rose up. They were the same living creatures that I had seen alongside the Kebar River/Canal.
Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
16 When the winged creatures moved, the wheels moved with them. When the winged creatures spread their wings to fly over the ground, the wheels did not leave them.
Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
17 When the winged creatures stopped, the wheels stopped. When the winged creatures started to fly, the wheels flew with them, because the spirit of the living creatures was in the wheels.
Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
18 Then the (glory/dazzling light) left the entrance of the temple and stopped above the winged creatures.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
19 While I watched, the winged creatures spread their wings and started to fly, and the wheels went with them. They stopped at the gate on the east side of the temple area, and the (glory/dazzling light) of God, the one whom the [had worshiped], was above them.
Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
20 Those were the [same] four living creatures that I had seen alongside the Kebar River/Canal, and I realized that they were the winged creatures.
Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
21 Each of them had four faces and four wings, and under their wings was what resembled a human’s hands.
Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
22 Their faces were the same as the faces that I had seen at the Kebar River/Canal. Each of them flew straight ahead.
Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.

< Ezekiel 10 >