< Exodus 1 >

1 The sons of Jacob who went to Egypt with him along with their families were
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2 Reuben, Simeon, Levi, Judah,
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3 Issachar, Zebulun, Benjamin,
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4 Dan, Naphtali, Gad, and Asher.
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5 Altogether there were 70 people [who went with] Jacob. That included his [sons, his grandsons, and two great-grandsons]. [His son] Joseph was already in Egypt.
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6 [Eventually] Joseph and his [older and younger] brothers and everyone [else in their family who lived] (in that generation/at that time) died.
Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7 But Jacob’s descendants kept giving birth to many children [IDM]. The number [of his descendants] kept becoming larger and larger. As a result, there were so many of them that they were everywhere in Egypt (OR, that they [became a threat] to the Egyptians).
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
8 Then [several hundred years later], a new king began to rule [MTY] in Egypt. He did not know [what] Joseph [had done for the people of Egypt long ago].
Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
9 He said to his people, “Look [at what has happened]! The Israeli people have become so numerous and so powerful that they [now might conquer] us!
Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
10 We must find a way to control them! If we do not do that, their population will continue to grow. Then, if enemies [PRS] attack us, they will join with our enemies and fight against us, and they will escape from [our] land.”
Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
11 So [the king and his officials] put supervisors over the Israeli people to cause them to suffer very much by [forcing them] to work very hard. They forced [the Israeli people to] build [two] cities, Pithom and Ramses, in which to store [supplies for the king/government].
Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
12 But the more cruelly they treated the [Israeli people], the bigger the Israeli [population] grew, and they became more numerous all over [the land]. So the Egyptian people began to be afraid of the Israeli people.
Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
13 They forced the Israeli people to work very hard,
ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
14 and by making them slaves, they made their lives miserable. They [forced them] to [build many buildings with] mortar and bricks. [They also forced them to do] other work in the fields. [In making them do all this work, the Egyptian officials treated them] ruthlessly/cruelly.
Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
15 There were two Hebrew (midwives/women who helped the women when they were giving birth). [Hebrew means the same as Israeli.] The names of the women were Shiphrah and Puah. The king of Egypt said to [those two women],
Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
16 “When you help the Hebrew women when they are giving birth [MTY], if [the baby that is born] is a boy, you must kill it. If [the baby] is a girl, you (may let it live/do not have to kill them).”
“Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
17 But the midwives feared/revered God. So they did not do what the king told them to do. They allowed the baby boys to live.
Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
18 So the king summoned the [two] midwives and said to them, “Why are you doing this? Why are you letting the baby boys live?”
Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
19 [One of] the midwives replied to the king, “[You need to realize that] the Hebrew women are not like the Egyptian women. The Hebrew women are very strong/healthy. They give birth [to their babies] before we can get to them [to help them].”
Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
20 So God acted kindly toward the midwives, and the [Hebrew] people became even more numerous and strong.
Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
21 Furthermore, because the midwives feared/revered God, he enabled them also to give birth to children.
Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
22 Then the king commanded all (the [Egyptian] people/his [advisors]): “You must throw into the Nile [River] every baby boy born that the [Hebrew women] give birth to! But you can allow the baby girls to live.”
Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”

< Exodus 1 >