< Exodus 9 >

1 Then Yahweh said to Moses/me, “Go to the king and say to him, ‘This is what Yahweh, the God [we] Hebrews [worship], says: “Allow my people to go, in order that they may worship me.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
2 If you still keep refusing to let them go [DOU],
In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
3 I warn you that I will punish you with my power [MTY] by sending a terrible disease on all your animals—on your horses, donkeys, camels, on your cattle, and on your flocks [of sheep and goats].
hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
4 But I, Yahweh, will distinguish between [what I do to] the animals that belong to the Israeli people and [what I do to] your animals. The result will be that no animal that belongs to the Israeli people will die.”’
Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
5 [Tell him that] I have determined/decided that tomorrow is the day that I will do this in this land.”
Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
6 The next day Yahweh did just what he said [that he would do]. A terrible disease afflicted all of the Egyptians’ animals, and many of them [HYP] died. But none of the Israeli people’s animals died.
Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
7 The king sent [men to investigate], and they were surprised [to see] that none of the Israeli people’s animals had died. But [after they reported that to] the king, he continued to be stubborn [IDM], and he did not let the [Israeli] people go.
Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
8 Then Yahweh said to Aaron and Moses/me, “Take a few handfuls of ashes/soot from (a furnace/an oven where they burn lime), and let Moses throw them up into the air, in front of the king.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
9 The [ashes/soot] will spread all over the country of Egypt like fine dust. And the ashes/soot will cause boils to afflict both the Egyptian people and their animals, all over the land.”
Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
10 So they/we both got some ashes/soot and [went and] stood in front of the king. Moses/I threw the ashes/soot up into the air. The ashes/soot spread all over, causing boils to afflict the [Egyptian] people and their animals. All the boils became open sores.
Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
11 Even the men who worked magic had boils. The result was that [they were suffering so much that] they were not able to come to Moses/me, because the men who worked magic had boils just like all [the rest of] the Egyptian people.
Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
12 But Yahweh caused the king to [continue to] be stubborn [IDM]. He did not pay any attention to what they/we [said], just as Yahweh had told Moses/me [would happen].
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
13 Then Yahweh said to Moses/me, “Get up early [tomorrow] morning. Go and stand in front of the king and tell him that Yahweh God, the one that the Hebrew people [worship], says this: ‘Let my people go, in order that they may worship me [in the desert].
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
14 [If you do not let them go], this time I will [punish] with plagues [not only] your officials and the rest of your people, but I will punish you yourself [SYN], in order that you will know there is no [god] like me anywhere in the world.
ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
15 By this time I could have used my power [MTY] to strike you and your people with terrible diseases that would have wiped you all from the earth.
Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
16 But I have let you live. The reason I have let you live is to show you my power, with the result that [people] all over the earth [HYP] will know how great I [MTY] am.
Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
17 You are still acting proudly and refusing to let my people go.
Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
18 So listen [to this]: About this time tomorrow I will cause very heavy hail to fall [in Egypt]. From the time Egypt first became [a country], there has never been a hailstorm [as bad as this one will be].
Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
19 So you should send [a message to everyone] to put their cattle, and everything else that they own that is [out] in the fields, under shelters. The hail will fall on every person and every animal that is out in the fields and that is not put under a shelter, and they will all die.’” [So Moses/I did what Yahweh said].
Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
20 Some of the king’s officials who heard what Yahweh had said became very afraid. So they put all their animals and their slaves under shelters.
Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
21 But those who did not pay any attention to what Yahweh had said left their slaves and their animals in the fields.
Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
22 Then Yahweh said to Moses/me, “Raise your hand up toward the sky, in order that hail will fall all over the land of Egypt—on the people and on their animals and on all the plants in the fields.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
23 So Moses/I lifted his/my stick up toward the sky. And Yahweh sent down hail, all over the land of Egypt. There was also thunder and lightning.
Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
24 While very heavy hail was falling, there was thunder, and lightning struck the ground. There had never been a hailstorm like that since Egypt first became a country.
ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
25 The hail struck everything that was in the fields all over Egypt—every person and every animal. The hail destroyed the plants in the fields and stripped [the leaves off] the trees.
Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
26 Only in the Goshen region, where the Israeli people were [living], was there no hail.
Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
27 Then the king sent [someone] to summon Aaron and Moses/me. [When they/we came to the king], he said to them/us, “This time [I admit that] I have sinned. What Yahweh [has done] is right, and what I and my people [have done] is wrong.
Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
28 (Pray to/Plead with) Yahweh [to cause it to stop]! [We] cannot [endure any more] of this thunder and hail! I will let your people go; they do not have to stay [here in Egypt] any longer.”
Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
29 Moses/I replied, “As soon as I go out of this city, I will lift up my hands [and pray] to Yahweh. Then the thunder will cease, and no more hail [will fall]. [This will happen] in order that you will know that Yahweh, [not your gods], controls everything [that happens] on the earth.
Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
30 But as for you and your officials, I know that you do not yet fear Yahweh God.”
Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
31 When the hail fell, the flax was ruined because the buds were forming, and the barley was ruined because its grain was ripe.
(Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
32 But none of the wheat crops was ruined, because their shoots were still very small.
Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
33 So Moses/I left the king and went outside the city. He/I lifted up his/my hands toward Yahweh [and prayed]. Then the thunder and the hail stopped, and the rain also stopped falling on the land [of Egypt].
Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
34 But when the king saw that the rain and the hail and the thunder had stopped, he sinned again. He and his officials continued to be stubborn [IDM].
Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
35 So, just as Yahweh had predicted by what he told Moses/me, the king did not allow the Israeli people to leave.
Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.

< Exodus 9 >