< Exodus 40 >
1 Then Yahweh said to Moses/me,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “On the first day of the first month next year, [tell the people to] set up the Sacred Tent.
“Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
3 Put inside it the sacred chest [that contains the stone slabs on which are engraved] the Ten Commandments, and hang the curtain in front of it.
Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
4 Bring the table into the Sacred Tent, and place on it all the things that are to be used with it. Bring in the lampstand and fasten the lamps to it.
Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
5 Put the gold altar for [burning] incense in front of the sacred chest, and set up the curtain at the entrance of the Sacred Tent.
Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
6 Put the altar for burning sacrifices in front of the Sacred Tent.
“Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
7 Put the washbasin between the Sacred Tent and the altar, and fill it with water.
ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
8 Hang the curtains that will surround the courtyard, and hang the curtain at its entrance.
Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
9 Then take the oil for anointing, and anoint the Sacred Tent and everything that is in it, to (set it apart/dedicate it) to me. Then it will be holy/sacred.
“Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
10 Also anoint the altar for offering sacrifices that will be completely burned, and all the things that will be used with it, and set it apart. Then it also will be holy/sacred.
Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
11 Also anoint the washbasin and its base, to set it apart.
Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
12 Then bring Aaron and his sons to the entrance of the Sacred Tent, and wash them [ritually] with water.
“Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
13 Then put on Aaron his sacred clothes to (set him apart/dedicate him), in order that he can serve me as a priest.
Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
14 Also bring his sons there. Put their sacred tunics/gowns on them
Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
15 and anoint them just as you anointed their father, in order that they also may serve me by working as priests. By anointing them [and their descendants], you will cause them and their descendants to be priests throughout all coming generations.”
Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
16 Moses/I did all these things exactly as Yahweh had commanded him/me.
Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
17 On the first day of the first month of the next year (OR, second year [after they/we left Egypt]), the people set up the Sacred Tent.
Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
18 Following Moses’/my instructions, they set up the Sacred Tent and its bases, set up the frames, attached the crossbars, and put up the posts [for the curtains].
Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
19 Then they spread out the coverings over the Sacred Tent, exactly as Yahweh had commanded.
Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
20 Then he/I took the two stone slabs [on which the commandments were written] and put them in the sacred chest. He/I put the carrying poles [in the rings] on the chest and put the lid on top of the chest.
Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
21 Then he/I took the chest into [the Very Holy Place inside] the Sacred Tent and hung the curtain. In that way, he/I prevented the people who were outside from seeing the chest. He/I did all this exactly as Yahweh had commanded him/me.
Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 He/I set the table inside the Sacred Tent, on the north side, outside the curtain.
Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
23 He/I placed on the table the bread that was offered to Yahweh, exactly as Yahweh had commanded.
Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
24 He/I set the lampstand inside the Sacred Tent, on the south side, opposite the table.
Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
25 Then he/I fastened the lamps to the lampstand in Yahweh’s presence, exactly as Yahweh had commanded.
ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
26 He/I set the golden altar for burning incense inside the Sacred Tent, in front of the curtain [that separated the Holy Place from the Very Holy Place],
Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
27 and he/I burned some sweet-smelling incense on it, exactly as Yahweh had commanded him/me.
ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
28 He/I hung the curtain at the entrance to the Sacred Tent.
Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
29 At the entrance to the Sacred Tent, he/I set the altar for offering sacrifices that were to be burned completely. Then he/I offered on it the meat that was to be burned completely and the grain offering, exactly as Yahweh had commanded him/me.
Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 He/I set the washbasin between the Sacred Tent and the [bronze] altar, and he/I filled the washbasin with water.
Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
31 Every time Moses/I and Aaron and his sons went into the Sacred Tent or went to the altar, they/we washed their/our hands and feet [ritually], exactly as Yahweh had commanded Moses/me.
a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
33 Following Moses’/my instructions, they hung the curtains that surrounded the courtyard and the altar, and they hung the curtain at the entrance to the courtyard. So Moses/I finished that work.
Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
34 Then the [tall bright] cloud covered the Sacred Tent, and Yahweh’s (glory/brilliant light) filled the Sacred Tent.
Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
35 Because that light was very bright, Moses/I was not able to enter the Sacred Tent.
Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
36 From that day, whenever the Israeli people wanted to move to another place, they went only when the bright cloud rose from above the Sacred Tent.
Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
37 If the cloud did not rise, they stayed where they were and did not go on until the cloud rose.
Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
38 Wherever they traveled, the bright cloud that [indicated] Yahweh’s [presence] was above the Sacred Tent during the day, and a [bright] fire was inside the cloud at night, with the result that all the Israeli people [MTY] could see it [at any time].
Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.