< Exodus 17 >
1 Obeying what Yahweh commanded, all the Israeli people moved from the Sin Desert. They/We traveled from one place to another. They/We camped at [a place named] Rephidim, but there was no water there for (the people/us) to drink.
Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
2 So the people complained to Moses/me again, saying, “Give us water to drink!” Moses/I replied to them, “Why are you (criticizing/arguing with) me [RHQ]? And why are you trying to determine whether Yahweh [has the power to provide for you]?”
Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
3 But the people were very thirsty, and they continued to complain to Moses/me. They were saying things like “Why did you bring us out of Egypt?”, and “Did you bring us here to cause us and our children and livestock to die (from thirst/because we had no water to drink) [RHQ]?”
Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
4 So Moses/I prayed earnestly to Yahweh. He/I said, “(How shall I deal with these people?/I do not know how to deal with these people!) [RHQ] They are almost ready to [kill me by throwing] stones at me!”
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
5 Yahweh replied to Moses/me, “Take some of the elders/leaders of the Israeli people with you and [tell the rest of] the people to follow you [to Sinai Mountain]. Take along the stick with which you struck the Nile [River].
Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
6 Listen carefully: I will stand in front of you on top of a [large] rock at the foot of the mountain. Strike the rock with your stick. [When you do that], water for the people to drink will flow out of the rock.” [When they/we arrived at the mountain], Moses/I did that while the Israeli elders were watching, [and water flowed from the rock].
Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
7 Moses/I gave that place two names [in the Hebrew language: ] Massah, [which means ‘testing’], and Meribah, [which means ‘complaining’]. He/I gave it the name Massah because the Israeli people were testing Yahweh, saying “Is Yahweh really among us [and able to help us], or not?”, and he/I gave it the name Meribah because they were [continually] complaining.
Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
8 Then the descendants of the Amalek people-group came and fought against the Israeli people at Rephidim.
Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
9 Moses/I said to Joshua, [who was one of our army/Israeli leaders], “Choose some men to go out and fight against the Amalek people-group tomorrow. I will stand on the top of the hill, holding the stick that God told me to carry.”
Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
10 So Joshua did what Moses/I told him to do. He took some men to fight against the Amalek people-group. [While they were fighting], Aaron, Hur, and Moses/I went up to the top of the hill [so that they/we could see the whole battle area].
Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
11 Whenever Moses/I lifted up his/my arms, the Israeli men started to win [the battle]. And whenever he/I lowered his/my arms, the Amalek people-group started to win.
Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
12 But his/my arms became tired. So Aaron and Hur [rolled] a [large] stone for Moses/me to sit on. [While he/I was sitting on it], those two held up his/my arms, [one on one side and the other on the other side]. In that way, they kept his/my arms lifted up, and his/my arms held steady until the sun went down.
Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
13 So Joshua and the men with him completely defeated the Amalek people-group, using their swords [to fight against them].
Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
14 Then Yahweh said to Moses/me, “Write an account of this battle, and then read it to Joshua. [Also write that some day] I will completely get rid of the Amalek people-group.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
15 Then Moses/I built a [stone] altar there and named it ‘Yahweh is [like] my flag’.
Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
16 He/I said, “Hold high Yahweh’s flag! Yahweh will continue to fight against the Amalek people-group (forever/in all future generations)!”
Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”