< Esther 7 >

1 So the king and Haman went to eat the second banquet/feast that Queen Esther had prepared.
Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
2 As they were drinking wine, the king asked again, “Esther, what do you want me to do [for you? Tell me, and] I will do it for you. Even if [you ask me for] half of my kingdom, I will give it to you.”
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
3 Esther replied, “O king, if you are pleased with me, and if you are willing to do [what I ask], save me, and save my people. That is what I want you to do for me.
Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
4 [It is as though] I and my people [are cattle that] have been sold to be slaughtered. [It is as though] we have been sold to people who want to completely destroy us. If we had only been sold to people to become their male and female slaves, I would not say anything, because that would have been a matter too small to bother you, the king.”
Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
5 Then King Xerxes asked her, “Who would want to do such a [terrible] thing? Where is he?”
Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
6 Esther replied, “[The man who is] our enemy is this evil man Haman!” Then Haman was terrified as he stood in front of the king and queen.
Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
7 The king became extremely angry. He immediately left his wine and got up and went outside into the palace garden [to decide what to do]. But Haman stayed, in order to plead with Queen Esther that she would spare his life.
Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
8 He threw himself down on the couch where Esther was reclining. But at that moment the king returned from the garden to the room where they had been eating. [He saw Haman, and assumed he was preparing to rape Esther]. He exclaimed, “Are you going to rape the queen while she is here with me in my own palace?” As soon as the king said that, some officials covered Haman’s head, [as they did to people who were about to be hanged].
Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
9 Then Harbona, one of the king’s personal officials, said, “[Outside, ] near Haman’s house, there is a (gallows/set of poles for hanging someone). It is 75 feet high. Haman made it for Mordecai, the man who spared your life!” The king said, “Hang him on it!”
Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
10 So they hanged Haman on the gallows that he had prepared for hanging Mordecai! And then (the king’s anger cooled off/the king was no longer so angry).
Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.

< Esther 7 >