< Deuteronomy 25 >

1 “If [two] Israelis have a dispute and they go to a court, the judge will [probably] decide/declare that one of them (is innocent/did not do any wrong) and the other one is guilty.
Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
2 If the judge says that the guilty person must be punished, he shall command him to lie [with his face] on the ground and be whipped. The number of times he is struck with a whip will depend on [what kind of] crime he committed.
in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
3 It is permitted that he be struck as many as 40 times, but no more than that. If he is struck more than 40 times, he would be humiliated publicly.
amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
4 When your ox is treading/walking on the grain [to separate the chaff from the grain], do not (muzzle it/put a covering on its mouth) [to prevent it from eating some of the grain].
Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
5 If two brothers live on the same property, and one of them who has no son dies, the man’s widow should not marry someone who is not a member of his family. The dead man’s brother must marry her and have sex [EUP] with her. It is his duty to do that.
In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
6 If she later gives birth to a son, that son is to be considered [MTY] the son of the man who died, in order that the dead man’s name will not disappear from Israel.
Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
7 “But if the dead man’s brother does not want to marry that woman, she must stand at the (gate/central meeting place) of the town and say to the [town] elders, ‘My husband’s brother will not do (his duty/what he is supposed to do). He refuses to [marry me in order that I may give birth to a son who will] prevent my dead husband’s name from disappearing in Israel.’
Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
8 Then the elders must summon that man and talk to him. If he still refuses to marry that widow,
Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
9 she must go up to him while the elders are watching, and take off one of his sandals [to symbolize/show that he would not receive any of her property], and spit in his face, and say to him, ‘This is what happens to the man who refuses to do what is needed [to allow his dead brother to have a son] in order that our family name does not disappear.’
sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
10 After that happens, that man’s family will be known as ‘the family of the man whose sandal was pulled off’.
Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
11 When [two] men are fighting with each other, and the one man’s wife comes near to help her husband by grabbing hold of the other man’s genitals,
In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
12 do not act mercifully toward her; cut off her hand.
sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
13 “[When you are buying or selling things], do not try to cheat people by having two kinds of weights, [one which you use when you buy something and one which you use when you sell something], and two kinds of measuring baskets, [one which you use when you buy something and one which you use when you sell something].
Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
15 Always use correct weights and correct measuring baskets, in order that Yahweh our God will allow you to live a long time in the land that he is giving to you.
Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
16 Yahweh hates all those who act dishonestly, [and he will punish them].
Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
17 Continue to remember what the Amalek people-group did to your ancestors when they were coming out of Egypt.
Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
18 They attacked your ancestors as your ancestors were traveling, when they were weak and exhausted. Those people were not afraid of God at all, so they attacked your ancestors from the rear and killed all those who were unable to walk as fast as the others.
Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
19 Therefore, when Yahweh our God has given you the land [that he promised to give you], and when he has enabled you to rest from [fighting] all your enemies around you, kill all the Amalek people-group, with the result that no one will remember them any more. Do not forget [to do this]!”
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!

< Deuteronomy 25 >