< Daniel 6 >

1 King Darius decided to divide his kingdom into 120 provinces. He appointed a governor to rule each province.
Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
2 He also appointed me and two other men to be administrators, to supervise the governors and to be sure that they did the king’s work [properly], in order that the king would not have to worry about anything.
ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
3 I soon showed that I was (more capable/able to do the work better) than all the other administrators and the governors. Because of that, the king planned to appoint me to be in charge of the entire empire.
To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
4 Then, the [other] administrators and the governors [became jealous. So they began to] try to find something that they could criticize about the way I was working for the king. But I always did my work faithfully and honestly, and was never lazy. So they could not find anything to criticize.
A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
5 They concluded, “The only way we can find something for which we can criticize Daniel will be something concerning the laws that his god [his given him].”
A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
6 So the administrators and governors went as one group to the king and said, “(Your Majesty/O king), we wish that you will live a long time!
Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
7 [We] administrators and governors and district governors and advisors and other officials have all agreed that you should make a law that everyone must obey. We want you to command that for the next thirty days people may pray only to you. If anyone prays to anyone else, either to a human or to a god, he must be thrown into [a pit of] lions.
Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
8 And because laws made by [our governments of] Media and Persia cannot be changed, [we want] you, [the head of our government], to sign it.”
Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
9 So King Darius [wrote] the law and signed it.
Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
10 But when I found out that [the king] had [written and] signed that law, I went home. I knelt down in my upstairs room and prayed. I looked toward Jerusalem, and the windows were open [with the result that everyone could see me while I was praying]. I prayed three times each day, just as I always did, thanking God.
To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
11 The officials went together [to my house] and they saw me praying and requesting God to help me.
Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
12 So they returned to the king and said to him, “[Do you remember] that you wrote a law stating that for the next thirty days people may pray only to you, and if anyone prays to anyone else, either to a human or to a god, he will be thrown into [a pit of] lions?” The king replied, “[Yes, that is the law that I wrote]. It is a law of [our governments of] Media and Persia, which cannot be canceled.”
Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
13 Then they said to the king, “Well, that [man] Daniel, one of the men who were brought from Judah, is not paying any attention to you or the law that you [signed]. He prays [to his god] three times each day!”
Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
14 When the king heard that, he was very distressed. He tried to find a way to save me. All the rest of that day he tried to think of a way to rescue me.
Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
15 [In the evening, many of] [HYP] the officials went together to the king and said, “(Your Majesty/O king), you know that [our governments of] Media and Persia have declared that no law that the king signs can be canceled/changed. [So Daniel must be thrown to the lions!]”
Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
16 So the king gave the order, and his servants brought me and threw me into a pit where the lions [were]. [Before they threw me in], the king said to me, “I hope/wish that your God, whom you worship regularly, will rescue you!”
Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
17 They rolled a huge stone across the entrance to the pit. Then the king [fastened a string across the entrance and put wax at each end, and stamped the wax with] the seal from his [ring] and the seals [of the rings] of his officials, in order that no one could [secretly] rescue me.
Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
18 Then the king returned to his palace. That night he refused to eat any food. He would not allow anyone to entertain him [because he did not want to be happy, with the result that he would forget about me. And that night] he was unable to sleep [because he was worried about me].
Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
19 At dawn the next morning, the king got up and went quickly to the pit where the lions were.
Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
20 When he came near it, he was very worried. He called out, “Daniel, you who serve the all-powerful God! Was your God, whom you worship regularly, able to save you from the lions?”
Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
21 I answered, “(Your Majesty/O king), I hope that you will live a long time!
Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
22 [Yes], my God sent his angel to shut the lions’ mouths, in order that they would not harm me! [He did that] because [he knows that] I have done nothing that he thinks is wrong. And, (Your Majesty/O king), I never did anything wrong to you!”
Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
23 The king was extremely happy, and he commanded [his servants] to lift me out of the pit. [When they did that, they] saw that the lions had not wounded me at all. [God had protected me] because I trusted in him.
Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
24 Then the king commanded that the men who had accused me should be seized and be thrown, along with their wives and children, into the pit where the lions were. [When they were thrown into the pit], the lions leaped on them and crushed their bones before they fell onto the bottom of the pit!
Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
25 Then King Darius wrote [this message and sent it throughout his kingdom] to the people of every people-group and nation and from all language groups: “I wish/hope that everything is going very well with you!
Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
26 I command that everyone in my kingdom should fear and revere the God that Daniel [worships]. He is the all-powerful God, and he will live forever. His kingdom will never be destroyed; he will rule forever.
“Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
27 He rescues and saves [his people]. He performs all kinds of miracles in heaven and on the earth. He rescued Daniel from the power of the lions!”
Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
28 So I was successful [all] during the time that Darius ruled and during the time that Cyrus, [the King] of Persia, ruled.
Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.

< Daniel 6 >