< Daniel 5 >

1 [Several years later, ] Belshazzar [became the] king [of Babylon. One day] he invited 1,000 of his officers to a big feast, and he drank [a lot of] wine with them.
Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
2 While he was drinking, he commanded [his servants] bring to him the gold and silver cups that the previous king, Nebuchadnezzar, had taken from the temple in Jerusalem. [He did that] because he wanted himself and his officials, his wives, and [even] his (concubines/slave wives) to drink from them, [making fun of the god that we Israelis worshiped].
Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
3 So his servants brought in [all] those gold cups, that had been taken [many years previously] from the temple of [the true] God in Jerusalem. Then the king and his officials and his wives and his slave wives drank [wine] from those cups.
Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
4 They drank to praise/honor their idols that were made of gold, silver, bronze, iron, and [even] wood and stone.
Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
5 Suddenly they saw a man’s hand writing on the plaster of the wall opposite the lampstand. The king also saw the hand as it was writing.
Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
6 He became very frightened, and his face became pale/white. His knees started shaking, and his legs became very weak, with the result that he could not stand up.
Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
7 [Then] he shouted to summon the men who worked magic, the men who studied the stars, and the fortune-tellers. He said, “I will [greatly honor] any one of them who can read this writing and tell me what it means. I will give him a purple [robe like I wear because I am the king], and I will put a gold chain around his neck. He will become a very important official in my kingdom; there will be only two others who will be more important than he will be.”
Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
8 But when all those wise men came in, none of them could read the writing, or tell him what it meant.
Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
9 So King Belshazzar became more afraid. His face became [even] paler/whiter. And [all] his officials [who were there at the feast] did not know what to do.
Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
10 But when the mother of the king (OR, of the previous king) heard the king and his officials talking [loudly about what had happened], she entered the room where they were having the feast. She said [to Belshazzar], “(Your majesty/O King), I hope you will live for a long time! But do not be pale and afraid about this.
Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
11 There is a man in your kingdom who has the spirit of the holy gods in him. When Nebuchadnezzar was ruling, they discovered that this man understood many things and was wise, just like the gods. The man who was king previously, Nebuchadnezzar, appointed him to be in charge of all the men [in Babylon] who worked magic, the men who worked sorcery, the men who studied the stars, and the fortune-tellers.
Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
12 That man’s name is Daniel; the king gave him a [new] name, Belteshazzar. He is very intelligent and is able to know and understand many things. He is [even] able to tell the meaning of dreams, and explain riddles, and explain things that are very difficult to understand. Summon him, and he will tell you what [this writing] means.”
Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
13 So they [went and] brought me in. The king asked me, “You [must] be Daniel [RHQ]! [They told me that you are] one of those who was brought [here] from Judah by the previous king.
Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
14 I have [also] heard that the spirit of the gods is in you, and that you are very wise and understand many things.
Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
15 My wise men and men who work magic have tried to read the writing on this wall and tell me what it means, but they are not able to do it.
An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
16 [Someone] told me that you can tell what dreams mean and explain things that are very difficult to understand. If you can read these words and tell me what they mean, [I] give you a purple robe [like I wear because I am the king], and I will put a gold chain around your neck. You will become a very important official in my kingdom; there will be only two others who will be more important than you will be.”
Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
17 I replied, “[I do not want] your gifts; keep them, or give them to someone else. But I will read for you the writing [on the wall], and I will tell you what it means.
Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
18 (Your Majesty/O king), the Supreme God caused the man who was king before you, Nebuchadnezzar, to become a great ruler, who was greatly praised and honored.
“Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
19 Because God caused him to become [very] great, people of many [HYP] people-groups and nations and who spoke many different languages were very much afraid of him. He [commanded his soldiers to] kill those whom he wanted to be killed, and he (spared/allowed to live) those whom he wanted to spare. He honored those whom he wanted to honor, and he caused to be disgraced those whom he wanted to be disgraced.
Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
20 But when he became very proud and stubborn [IDM], he was removed from being king [MTY]. People did not consider him to be glorious/great any more.
Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
21 [His officials] sent him away in order that he would not be near [other] people. [God] caused him to have a mind like animals have. He lived among the wild donkeys. He ate grass like cows do, and dew from the sky caused his body to be damp/wet [each morning]. [He was like that] until he learned that the Supreme God is [really the one who] rules the kingdoms of this world, and that he appoints whomever he chooses to rule those kingdoms.
Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
22 Now, Belshazzar, you have become the king. You [also] knew all those things, but you have not made yourself humble.
“Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
23 You have considered yourself to be greater than [God], the Lord of heaven. [So you have commanded your servants to] bring to you these sacred cups, [which were dedicated to the Supreme God, and which were taken] from his temple [in Jerusalem]. You and your officials and your wives and your (concubines/slave wives) have been drinking wine from these cups, while you have been praising [your own] gods—gods which are made of gold and silver and bronze and iron and wood and stone. [Those are gods] that cannot see, that cannot hear, and that do not know anything! You have not honored the God who gives you breath and who controls everything that happens to you.
A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
24 So God sent that hand to write a message [for you].
Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
25 This is the message that it wrote: ‘Mene, mene, tekel, parsin.’
“Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
26 This is what those words mean: Mene [means] ‘numbered/counted’. [That means that] God has been counting the days that you will rule, and he has [now] decided that you will not rule any more.
“Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
27 Tekel [means ‘weighed’. It is as though God] has weighed you on a scale, and you do not weigh what you should, [which means that you have not been doing what you should; you are not fit to be a king] [MET].
“Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
28 Parsin [means ‘divided’. That means that God] has divided your kingdom. Some of it will be ruled by people from Media and some will be ruled by people from Persia.”
“Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
29 Then Belshazzar [did what he had promised]. He put on me a purple robe [like the one he himself wore. He] put a gold chain around my neck. And he proclaimed that there would be only two others who would be more important than me in his kingdom.
Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
30 But that same night [soldiers from Media entered the city and] killed Belshazzar, the King of Babylonia.
A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
31 Darius, the King of Media, became the King [of Babylonia] when he was 62 years old.
Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.

< Daniel 5 >