< Daniel 2 >

1 [One night] during the second year that Nebuchadnezzar ruled, he had a dream. The dream worried him very much; and [as a result] he could not sleep.
A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
2 [The next morning] he summoned his men who worked magic, fortune-tellers, those who worked sorcery, and those who studied the stars. [Because he had forgotten what he had dreamed, ] he insisted that they tell him what he had dreamed. As they stood there in front of the king,
Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
3 he said, “I had a dream [last night] that worries me. [Tell me what I dreamed, because] I want to know what the dream [means].”
sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
4 The men who studied the stars replied to the king, speaking in the Aramaic [language]. They said, “King Nebuchadnezzar, we hope that you will live a long time! Tell us what you dreamed, and [then] we will tell you what it means!”
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
5 But the king replied, “I have firmly decided that you must tell me the dream, and [also tell me] what it means. If you do not do that, I will [order my soldiers to] cut you into pieces, and to cause your houses to become only piles of stones!
Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
6 But if you tell me what I dreamed and what it means, I will reward you. I will give you wonderful gifts and greatly honor you. So tell me what I dreamed and what it means!”
Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
7 But again they said, “Tell us what you dreamed, and [then] we will tell you what it means.”
Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
8 The king replied, “I know that you are just trying to get more time, because you know that I will do to you what I said that I would do.
Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
9 If you do not tell me what I dreamed, you will be punished. [I think that] you have all agreed to tell me lies and [other] wicked things, because you hope that I will change ([my mind/what I am thinking]). But tell me the dream, and [then] I will know that you can [also] tell me what it means.”
In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
10 The men who studied the stars replied, “There is no one on the earth who can do what you ask! There is no king, [even] a great and mighty king, who has [ever] asked his men who work magic or his fortune-tellers or men who study the stars to do something like that!
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
11 What you are asking [us to do] is impossible. Only the gods can tell you what you dreamed, and they do not live among us!”
Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
12 The king was very angry when he heard that, so he commanded [his soldiers] that they execute all such wise men in Babylon.
Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
13 And because of what the king commanded, they sent some men to find me and my [three] friends, to execute us [also].
Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
14 Arioch, the commander of the king’s guards, came to kill us. But I spoke to him very wisely and tactfully/skillfully.
Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
15 I asked Arioch, “Why has the king made such a harsh/terrible decree?” So Arioch told me all that had happened [because of the king’s dream].
Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
16 I [immediately] went to talk to the king and requested that the king give me some time, so that I could find out [what the dream was and] what the dream meant.
Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
17 Then I went home, and I told my friends, Hananiah, Mishael, and Azariah, what had happened.
Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
18 I urged them to ask God, who lives/rules in heaven, to have mercy on us by telling us the secret [meaning of what the king dreamed], in order that we and the other wise men in Babylon would not be executed.
Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
19 And that night [God] gave to me a vision in which he revealed the secret. Then I praised God,
A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
20 saying, “We should praise God [MTY] forever, because [only] he truly is wise and powerful.
Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
21 He determines what events will happen through the years. He removes [some] kings and gives their authority to [new] kings. He is the one who causes people to become wise and enables those who study to understand [many] things.
Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
22 He reveals things that are very mysterious; he is surrounded by light, but he knows things that are hidden [as though they were] in the darkness.
Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
23 God, whom my ancestors [worshiped], I thank you and I praise you, because you have caused me to be wise and made me strong. You have told me what my friends and I asked you to tell us; and you have revealed to us what the king demanded to know.”
Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
24 Then I went to Arioch, the man whom the king had appointed to execute the wise men in Babylon. I said to him, “Do not kill those wise men. Take me to the king, and I will tell him what his dream means.”
Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
25 So Arioch quickly took me to the king. He said to the king, “I have found [this man], one of the men whom we brought from Judah who [says he can] can tell you what your dream means!”
Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
26 The king said to me, whose [new] name was Belteshazzar, “[Is this true]? Can you tell me what I dreamed and what it means?”
Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
27 I replied, “There are no wise men or fortune-tellers or men who work magic or men who work sorcery who can tell such things to you.
Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
28 But there is a God in heaven who reveals secrets. And he has shown in [your dream] what will happen in the future. Now I will tell you what you dreamed, the vision you saw [as you were lying] on your bed.
amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
29 O King, while you were sleeping, you dreamed about events that will happen in the future. The one who reveals mysteries has shown you what is going to happen.
“A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
30 And it is not because I am wiser than anyone else on earth that I know the meaning of this mysterious dream. It is because God wanted you to understand what you were thinking.
Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
31 O King, [in your vision] you saw in front of you a huge and terrifying statue [of a man. It was] shining very brightly, and it was frightening and awesome.
“Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
32 The head of the statue was [made] of pure gold. Its chest and arms [were made of] silver. Its belly and thighs [were made of] bronze.
An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
33 Its legs [were made of] iron, and its feet were a mixture of clay and iron.
An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
34 As you watched, something cut a rock [from a mountain, but it was] not a human [who cut it]. The rock [tumbled down and] smashed the feet of the statue, feet [that were made of] iron and clay. It smashed them to bits.
A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
35 Then the rest of the statue collapsed into a big heap of iron, clay, bronze, silver, and gold. The pieces of the statue were as small as bits of chaff on the ground where it is threshed, and the wind blew away all the tiny pieces. There was nothing left. But the rock that smashed the statue became a large mountain that covered the whole earth.
Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
36 That was what you dreamed. Now I will tell you what it means.
“Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
37 You are a king [who rules] over [many other] kings. The God who rules in heaven has caused you to rule over them and has given you great power [DOU] and has honored you.
Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
38 He has caused you to be the ruler over all people, and [even] the animals and birds are controlled by you. [So] the head [of the statue] represents you.
a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
39 But after your [kingdom/rule] ends, there will be another [great] kingdom, [but it] will not be as great as yours. [The silver parts of the statue represent that kingdom]. Then there will be a third [great] kingdom [whose king] will rule over the whole earth. The bronze parts [of the statue represent] that kingdom.
“A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
40 After that kingdom ends, there will be a fourth [great] kingdom. The iron [parts of the statue represent that kingdom]. [The army of] that kingdom will smash the previous kingdoms, just like iron smashes everything that it strikes.
A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
41 The feet and toes of the statue that you saw, that were a mixture of iron and clay, indicate that the kingdom they represent will [later] be divided.
Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
42 Some parts of that kingdom will be as strong as iron, but some parts will not remain together, just as iron and clay do not stick together.
Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
43 The mixture of iron and clay [in the statue] shows also that the rulers of those kingdoms that separate from each other will try to form alliances with each other as a result of members of the royal families of those kingdoms marrying each other. But that will not succeed, just as iron and clay do not stick together.
Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
44 But while those kings are ruling, God who rules in heaven will establish a kingdom that will never end. No one will ever defeat its king. He will completely destroy all those kingdoms, but his kingdom will remain forever.
“A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
45 That is the meaning of the rock that something cut from the mountain, the rock that will crush to tiny bits the statue that is made of iron, bronze, silver, and gold. O king, the great God has shown you what will truly happen in the future. And you can trust [what I told you about] the meaning of the dream.”
Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
46 Then King Nebuchadnezzar prostrated himself in front of me [in great respect]. He commanded [his people] that they burn incense and burn an offering of grain to honor me.
Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
47 The king said to me, “[Your God has enabled] you to tell me the meaning of this dream/mystery, so now I truly know that your God is greater than all the other gods and all other kings. He reveals [to people] things that they cannot know.”
Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
48 Then the king gave many gifts to me, and he [also] appointed me to rule over the entire province of Babylon, and [also] to be the boss of all his wise men.
Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
49 I asked the king to appoint Shadrach, Meshach, and Abednego to [also] have important positions in Babylon province, and the king did what I asked him to do. But [I did my work while] I stayed at the king’s palace.
Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.

< Daniel 2 >