< Daniel 12 >

1 [The angel also said to me, ] “After those things happen, the great angel Michael, who protects the [Israeli] people, will appear. Then there will be a time when there will be great troubles/suffering. The troubles will be greater than any troubles/suffering since the nations began. At that time, all of your people whose names have been written in the book [containing the names of those who have eternal life] will be saved.
“A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
2 Many of those who have died [EUP] will become alive again. Some of them will live eternally [with God], and some will be eternally shamed/disgraced [in hell]. (questioned)
Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
3 Those who were wise will shine as brightly as the sky [is bright when the sun is shining]. And those who have shown to others the way to live righteously will shine forever, like the stars [SIM].
Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
4 But as for you, Daniel, close up the scroll [on which you are writing], and seal it [in order that no one can open it] until the end [of the world] is near. [Before that happens, ] many people will travel rapidly here and there, learning more and more [about many things].”
Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
5 When [that angel finished speaking], I, Daniel, looked up, and suddenly I saw two other [angels]. One was standing on the side of the river [where I was], and one was standing on the other side.
Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
6 One of them [called to] the other one, who was wearing linen/white clothes, who was now standing further up (OR, above) the river, “How long will it be until these amazing/frightening events end?”
Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
7 The angel who was on the other side of (OR, above) the river raised his hands toward the sky, and solemnly promised, with the authority [MTY] of God, who lives forever, “It will be three and a half years. All these things will end after God’s people stop fighting against those who (persecute/cause trouble for/cause suffering for) them.”
Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
8 I heard [what he said], but I did not understand it. So I asked, “Sir, what will be the result when these things end?”
Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
9 He replied, “Daniel, you must leave now. [I cannot answer your question] because what it means must (be kept secret/not be revealed) [DOU] until the time when everything ends.
Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
10 Many people will thoroughly purify their inner beings [DOU]. But wicked people will not understand these things. They will continue to be wicked. Only those who are wise will understand [these things].
Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
11 [But I can tell you that before everything ends, ] there will be 1,290 days, from the time that people are prevented from offering sacrifices each day, that is, from the time that the abominable/disgusting thing is put in the temple.
“Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
12 God will be pleased with those who remain faithful until 1,335 days are ended.
Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
13 So [now I say] to you, continue to faithfully [trust God] until [your life on earth] ends. You will die [EUP], but when everything ends, you will receive your reward [from God].”
“Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”

< Daniel 12 >