< 2 Samuel 5 >

1 Then [the leaders of] all the tribes of Israel came to David at Hebron, and said to him, “Listen, we have the same ancestors [IDM] that you do.
Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
2 In the past, when Saul was our king, it was you who led our Israeli soldiers [in our battles]. You are the one to whom Yahweh promised, ‘You will be the leader [MET] of my people; you will be their king.’”
A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
3 So while Yahweh was listening, all those leaders of the people of Israel declared there at Hebron [that David would be their king]. And David made a sacred agreement with them. They anointed him [with olive oil to set him apart] to be the king of the Israeli people.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
4 David was 30 years old when he became their king. He ruled them for 40 years.
Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
5 In Hebron he ruled over the tribe of Judah for seven and a half years, and in Jerusalem he ruled over all the people of Judah and Israel for 33 years.
A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
6 [One day] King David and his soldiers went to Jerusalem to fight against the Jebus people-group who lived there. The people there thought that David’s army would not be able to capture the city, so they sent a message to David, saying “Your army will never be able to get inside our city! Even the blind and crippled people will be able to chase you away!”
Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
7 But David’s army captured the fortress on Zion [Hill], [and later it was known as] David’s City.
Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
8 On that day, David said [to his soldiers], “Those who want to get rid of the Jebus people-group should go through the water tunnel [to enter the city]. Then they can attack those people whom I [SYN] detest—[and we will find out if any] blind and crippled people [will be able to stop them]!” That is why people say, “Blind and crippled people cannot enter Yahweh’s temple.”
A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
9 [After] David [and his soldiers captured] the city with its strong walls around it, he lived there, and they named it ‘David’s City’. David [and his soldiers] built the city around the fortress, starting where the [land was (filled in/terraces) on the east side of the hill].
Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
10 David continued to become more and more powerful/influential, because the Almighty Commander of the armies of angels was with/helping him.
Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
11 [One day] Hiram, the king of Tyre [city], sent ambassadors/messengers to David [to talk about making agreements between their countries]. Hiram agreed to provide cedar trees [to make lumber], and also that he would send carpenters and masons, to build a palace for David.
To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
12 His doing that caused David to realize that Yahweh truly had appointed him to be the king of Israel, and that Yahweh was going to cause his kingdom to prosper, because Yahweh loved the Israeli people, whom [he had chosen to] belong to him.
Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
13 After David moved from Hebron to Jerusalem, he took more slave women to be his second-class wives, and he also married other women. [All of those women] gave birth to more sons and daughters.
Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
14 The names of the sons who were born in Jerusalem were Shammua, Shobab, Nathan, Solomon,
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
15 Ibhar, Elishua, Nepheg, Japhia,
Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
16 Elishama, Eliada, and Eliphelet.
Elishama, Eliyada da Elifelet.
17 When the Philistia people heard that David had been appointed to be the king of Israel, their army went up [toward Jerusalem] to try to capture David. But David heard that they were coming, so he went down to another fortified place.
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18 The [army of] Philistia arrived at Rephaim Valley [southwest of Jerusalem] and spread all over the valley.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19 David asked Yahweh, “Should [my men and] I attack the Philistia army? Will you enable us to defeat them [IDM]?” Yahweh replied, “Yes, attack them, because I will certainly enable your army to defeat them. [IDM]”
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20 So David [and his army] went to [where the Philistia army was], and there they defeated them. Then David said, “Yahweh has burst through my enemies like a flood.” [SIM] So that place is called ‘Lord of Bursting-through’.
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21 The Philistia men left their idols there; so David and his soldiers took them away.
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
22 Then the Philistia [army] returned to Rephaim Valley and spread all over the valley.
Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
23 So again David asked Yahweh [if his army should attack them]. But Yahweh replied, “Do not attack them [from here]. Tell your men to go around them and attack them from the other side, near the balsam trees.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
24 When you hear something in the tops of the balsam trees that sounds like [an army] marching, attack them, because I will have gone ahead of you [to enable your army] to defeat their army.”
Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
25 So David did what Yahweh told him to do, and his [army] defeated the Philistia army from Geba [city] all the way [west] to Gezer [city].
Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

< 2 Samuel 5 >