< 2 Samuel 4 >

1 When Saul’s son Ishbosheth heard that Abner had been killed at Hebron, [he realized that he might also be killed]. He became discouraged, and all the Israeli people (trembled/became afraid).
Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
2 Ishbosheth had two officers who were leaders of groups that raided other villages. [They were brothers; ] their names were Baanah and Rechab, sons of Rimmon from Beeroth [town] in the tribe of Benjamin. Beeroth is in the area that had [been assigned to] the tribe of Benjamin.
To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
3 But the people of Beeroth had fled to Gittaim [town], and they still live there.
domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
4 Saul’s son Jonathan had a son named Mephibosheth. When Mephibosheth was five years old, Saul and Jonathan died in the battle. When people brought that news from Jezreel, Mephibosheth’s nursemaid picked him up and ran away. She ran very fast, with the result that she dropped him, and his legs became crippled.
(Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
5 One day, Rechab and Baanah left [their home] to go to Ishbosheth’s house. They arrived there about noontime, when Ishbosheth was taking his midday nap.
To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
6 The woman who was the doorkeeper was sifting wheat. While doing that, she became sleepy, and fell asleep. So Rechab and his brother Baanah were able to creep in quietly.
Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
7 They entered Ishbosheth’s bedroom, where he was sleeping. They killed him [with their swords] and cut off his head. They carried his head and walked all night through the Jordan [River] Valley.
Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
8 They took the head of Ishbosheth to David at Hebron. They said to him, “Here is the head of Ishbosheth, the son of your enemy Saul, who tried to kill you. Your majesty, today Yahweh has allowed you to get revenge on Saul and his descendants!”
Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
9 But David replied to them, “Yahweh is the one who has rescued me from all my troubles. And just as surely as Yahweh lives, what I am now saying is also true.
Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
10 When a messenger came to Ziklag and told me ‘Saul is dead!’ and he thought that the news that he was bringing to me was good news, I seized him and [commanded one of my soldiers to] kill him. That was the reward I gave to him for his news!
sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
11 So because you two evil men murdered a man who is (innocent/has done nothing wrong) when he was sleeping on his bed in his own house, I will do something worse to you. I will surely [RHQ] get revenge on you two for murdering [MTY] him, and (wipe you/cause you to disappear) from the earth!”
Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
12 Then, following David’s orders, his soldiers killed the two men, and cut off their hands and their feet, and hung their bodies (OR, their hands and feet) [on a pole] near the pool at Hebron. But they took the head of Ishbosheth and buried it [respectfully] in the tomb of Abner, there at Hebron.
Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.

< 2 Samuel 4 >