< 2 Samuel 23 >

1 David, the son of Jesse, was a man whom [God caused to] become great. He was appointed to become king by the God whom Jacob [worshiped]. He wrote beautiful songs for the Israeli people. This is the last song that he wrote:
Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
2 “The Spirit of Yahweh tells me what to say; the message that I speak [MTY] comes from him.
“Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
3 God, the one whom we Israeli [people worship], has spoken; the one who protects us Israeli people said to me, ‘Kings who rule people justly have an awesome respect for me, God.
Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
4 They are like the sun that shines at dawn and causes the grass to [sprout/sparkle] after the rain ends.’
yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
5 And truly, that is how God will surely bless my family [RHQ] because he made an agreement with me that will endure forever, an agreement in which he promises that no part of it will ever be changed. He will surely cause me to prosper [RHQ], and he will always help me, and that is all that I desire.
“Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
6 But [he will get rid of] godless/evil people like [SIM] people throw away thorns that [injure people if they try to] pick them up with their hands.
Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
7 Someone [who wants to get rid of thornbushes] does not grab them; he uses an iron [shovel] or a spear [to dig them out] and then he burns them completely.
Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
8 These are the names of David’s three greatest warriors. The first was Esh-Baal, [whose other name was Jashobeam], from the Hachmon clan (OR, the son of Hachmon). He was the leader of the three men. One time he fought against 800 enemies and killed them all with his spear.
Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
9 The second/next one of the three greatest warriors was Eleazar, who was the son of Dodo from the clan of Ahoh. One day he was with David when they defied/challenged the soldiers of Philistia who had gathered for the battle. The [other] Israeli soldiers retreated,
Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
10 but Eleazar stood there and fought the soldiers of Philistia until his arm became very tired, with the result that [his hand cramped and] he could not stop gripping his sword. Yahweh won a great victory on that day. And afterwards the [other] Israeli soldiers returned [to where Eleazar was], and stripped off the [armor from the men whom he had] killed.
amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
11 The third one of the greatest warriors was Shammah, the son of Agee from [the clan/town of] Harar. One time the Philistia soldiers gathered at Lehi [town], where there was a field full of lentils/peas [that they wanted to steal]. The other Israeli soldiers ran away from the Philistia troops,
Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
12 but Shammah stood there in the field and did not let the Philistia soldiers [steal the crops], and killed them. Yahweh won a great victory on that day.
Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
13 Altogether there were 30 special warriors among David’s soldiers. Once, when it was almost time to harvest [the crops], three of those 30 men went down to Adullam Cave, where David was [staying]. A group of men from the Philistia army had set up their tents in Rephaim Valley [near Jerusalem].
A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
14 David [and his soldiers] were in the cave [because it was safe there], and [another] group of Philistia soldiers was occupying Bethlehem.
Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
15 [One day] David very much wanted [some water] to drink, and said “I wish that someone would bring me some water from the well near the gate at Bethlehem!”
Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
16 So his three greatest warriors forced their way through the camp of Philistia soldiers and drew some water from the well, and brought it to David. But he would not drink it. Instead, he poured it out [on the ground] as an offering to Yahweh.
Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
17 He said, “Yahweh, it would certainly not be right for me to drink this water! That would be like [RHQ] drinking the blood of these men who were willing/ready to die for me!” So he refused to drink it. That was one of the things that those three great warriors did.
Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
18 Abishai, Joab’s [younger] brother, was the leader of the 30 [greatest warriors]. [One day] he fought against 300 men and killed them all with his spear. As a result, he also became famous.
Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
19 He was the most famous of the thirty greatest warriors, and he became their leader/commander, but he was not one of the three greatest warriors.
Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
20 Jehoiada’s son Benaiah, from Kabzeel [town], also did great deeds. He killed two of the best warriors from the Moab people-group. Also, he went down into a pit on a day when snow was falling, and killed a lion there.
Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
21 He also killed a huge soldier from Egypt who carried a spear. Benaiah [had only] his club, but he attacked the giant with it. Then he snatched the spear from the man’s hand and killed him with his own spear.
Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
22 Those are [some of] the things that Benaiah did. As a result, he became famous, like the three greatest warriors were.
Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
23 He was more honored than the other members of the group of thirty great warriors, but not as famous as the three greatest warriors. David appointed him to be the commander of his bodyguards.
Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
24 [These are the names of the great warriors]: Asahel, the brother of Joab; Elhanan, the son of Dodo, from Bethlehem;
Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
25 Shammah and Elika, from [the] Harod [clan];
Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
26 Helez, from Pelet [city]; Ira, the son of Ikkesh, from Tekoa [town];
Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
27 Abiezer, from Anathoth [city]; Mebunnai [whose other name was Sibbecai], from Hushah’s [clan];
Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
28 Zalmon [whose other name was Ilai], from Ahoh’s [clan]; Maharai, from Netophah [town];
Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
29 Heleb, the son of Baanah, also from Netophah [town]; Ittai, the son of Ribai, from Gibeah [town] in [the land that belonged to] the tribe of Benjamin;
Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
30 Benaiah, from Pirathon [town]; Hiddai, from the valleys near Gaash [Mountain];
Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
31 Abi-Albon, from the clan of Arabah; Azmaveth, from Bahurim [town];
Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
32 Eliahba, from Shaalbon [town]; The sons of Jashen; Jonathan;
Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
33 Shammah, from Harar [town/clan]; Ahiam the son of Sharar, from Harar [town/clan];
ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
34 Eliphelet, the son of Ahasbai, from Maacah [town]; Eliam, the son of Ahithophel, from Gilo [town];
Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
35 Hezro, from Carmel [city]; Paarai, from Arba [city];
Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
36 Igal, the son of Nathan, from Zobah [city]; Bani, from the tribe of Gad;
Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
37 Zelek, from the Ammon people-group; Naharai, the man who carried Joab’s weapons, from Beeroth [town];
Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
38 Ira and Gareb, from Jattir [town];
Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
39 Uriah, [Bathsheba’s husband], from the Heth people-group. Altogether, there were 37 famous soldiers, [but some of them had died and their names were not included].
da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.

< 2 Samuel 23 >