< 2 Samuel 20 >

1 There was a man there [at Gilgal] named Sheba. He was a man who always caused trouble. He was from the tribe of Benjamin and was the son of Bichri. He blew a trumpet and called out, “We have nothing to do with [DOU] David, that son of Jesse! So, men of Israel, let’s go to our homes!”
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 So all the men from the other Israeli tribes deserted David and went with Sheba, but the men of Judah stayed with David. They wanted him to be their king, and went with him from near the Jordan [River] up to Jerusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 When David arrived at the palace in Jerusalem, he took the ten slave wives whom he had left there to take care of the palace and put them in another house. He put a guard at that house, and he provided for them what they needed, but he never had sexual relations [EUP] with them again. So they remained shut up in their house until they died. It was as though they were widows.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 [One day] the king said to Amasa, “Summon the soldiers of Judah to come here within three days, and you be here also.”
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 So Amasa went to summon them, but he did not return within the time that David told him to.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 So David said to Abishai, “Now Sheba will harm us more than Absalom did. So you take my soldiers and pursue him. If you do not do that, he and his soldiers may occupy/capture some of the (fortified towns/towns that have walls around them), and escape from us. [IDM]”
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 So Abishai [and Joab] and the king’s bodyguards and the other soldiers left Jerusalem, to pursue Sheba.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 When they arrived at the huge rock in [the] Gibeah [region], Amasa met them. Joab was wearing a soldier’s uniform. He had a dagger/long knife fastened to his belt. When he came close [to Amasa, he allowed] the dagger [to] fall on the ground.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 Joab said to Amasa, “Are things going well with you, my friend?” Then Joab grabbed Amasa’s beard with his right hand, in order to kiss him.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 But Amasa did not see that Joab was holding [another] dagger in his [other] hand. And Joab stabbed it into Amasa’s belly, and his insides spilled out onto the ground. Amasa died [immediately]; Joab did not need to stab him again. Then Joab and his brother Abishai continued to pursue Sheba.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 One of Joab’s soldiers stood alongside Amasa’s body and called out, “Everyone who wants Joab [to be our commander] and who wants David [to be our king], go with Joab!”
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 Amasa’s body was lying on the road. It was covered with blood. The soldier of Joab [who had called out] saw that many others of Joab’s soldiers were stopping [to see it], so he dragged Amasa’s body off the road into a field, and threw a cloth/blanket over the body.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 After the body had been taken off the road, all the soldiers went with Joab to pursue Sheba.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 Sheba went through all the tribes of Israel, and arrived at Abel-Beth-Maacah [town in the northern part of Israel]. There, all the members of [his father] Bichri’s clan gathered, and went with Sheba into the town.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 The soldiers who were with Joab [found out that Sheba had gone there, so they] went there and surrounded the town. They built a dirt ramp up against the town wall. They also pounded against the wall [with heavy poles], to cause it to collapse.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 Then a wise woman who was in that town [stood on the top of the wall and] shouted down, “Listen to me! Tell Joab to come here, because I want to talk to him!”
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 So [after they told Joab], he came there, and the woman said, “Are you Joab?” He replied, “Yes, I am.” She said to him, “Listen to what I say.” He replied, “I am listening.”
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 She said, “Long ago people used to say, ‘Go to Abel [town] to get good advice about your problems.’ And that is what people did.
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 We are peaceful and loyal Israelis. Our people here are important and respected [IDM]. So (why are you trying to destroy a town that belongs to Yahweh?/you should not be trying to destroy a town that belongs to Yahweh.)” [RHQ]
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 Job replied, “I would certainly never want to ruin or destroy your town!
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 That is not what we want to do. But Bichri’s son Sheba, a man from the hilly area in the tribe of Ephraim, is rebelling against King David. Put this man into our hands, and then we will (go away from/not attack) this town.” The woman replied to Joab, “Okay, what we will do is, we will [cut off] his head [and] throw it over the wall to you.”
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Then this wise woman went to the elders of the town and told them what she had said to Joab. So they cut off Sheba’s head and threw it over the wall to Joab. Then Joab blew his trumpet [to signal that the battle was ended], and all his soldiers left the town and returned to their homes. And Joab returned to Jerusalem and told the king [what had happened].
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Joab was the commander of the entire Israeli army. Jehoiada’s son Benaiah was the commander of David’s bodyguards;
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 Adoram supervised the men who were forced to work [for the king]; Ahilud’s son Jehoshaphat was the man who reported [to the people everything that David decided];
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 Sheva was the official secretary; Zadok and Abiathar were the priests;
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 and Ira from Jair [town] was also one of David’s priests.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.

< 2 Samuel 20 >