< 2 Kings 25 >
1 On January 15 of the ninth year that Zedekiah had been ruling, King Nebuchadnezzar arrived with his whole army, and they surrounded Jerusalem. They built ramps [made of dirt against the walls of the city], so that they could climb up the ramps and attack the city.
A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
2 They did that for two years.
Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
3 After Zedekiah had been ruling for eleven years, the (famine/shortage of food) had become very bad. All their food was gone.
A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
4 On July 18 of that year, the Babylonian soldiers broke through part of the city wall, [and that enabled them to enter the city]. All the soldiers of Judah [wanted to escape]. But the Babylonian soldiers surrounded the city, so the [king and] the soldiers of Judah waited until it was nighttime. Then they fled through the gate that was between the two walls near the king’s park. They ran across the fields and started to go down to the Jordan [River] Valley.
Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
5 But the Babylonian soldiers chased/ran after them. They caught the king when he was by himself in the valley near the Jordan River. He was by himself because all his soldiers had abandoned him.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
6 The Babylonian soldiers took King Zedekiah to Riblah [city] in Babylon. There the king of Babylon decided what they would do to punish him.
Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
7 There the king of Babylon forced Zedekiah to watch as the Babylonian soldiers killed all of Zedekiah’s sons. Then they gouged out Zedekiah’s eyes. They put bronze chains on [his hands and feet] and then they took him to Babylon.
Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
8 On August 14 of that year, after Nebuchadnezzar had been ruling for 19 years, Nebuzaradan arrived in Jerusalem. He was one of king Nebuchadnezzar’s officials and captain of the men that guarded the king.
A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
9 He [commanded his soldiers to] burn down the temple of Yahweh, the king’s palace, and all the houses in Jerusalem. So they burned down all the important buildings in the city.
Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
10 Then Nebuzaradan supervised all the soldiers of the Babylonian army as they tore down the walls of Jerusalem.
Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
11 Then he and his soldiers took to Babylon the people who were still living in the city, the other people [who lived in that area], and the soldiers who had previously surrendered to the Babylonian army.
Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
12 But Nebuzaradan allowed some of the very poor people to stay in Judah to take care of the vineyards and [to plant crops in] the fields.
Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
13 The Babylonian soldiers broke into pieces the bronze pillars, the bronze carts with wheels, and the huge bronze basin, all of which were in the temple courtyard, and they took all the bronze to Babylon.
Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
14 They also took the pots, the shovels, the instruments for (snuffing out/extinguishing) [the wicks of] the lamps, the dishes, and all the other bronze items that the Israeli priests had used for offering sacrifices at the temple.
Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
15 The soldiers also took away the (firepans/trays for carrying burning coals), the basins, and [all the other] items made of pure gold or pure silver.
Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
16 The bronze from the two pillars, the carts with wheels, and the huge basin were very heavy; they could not be weighed. (Those things had been made/A man named Hiram had made these things) for the temple when Solomon [was the king of Israel].
Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
17 Each of the pillars was (27 feet/8 meters) tall. The bronze capital/top of each pillar was (7-1/2 feet/2.3 meters) high. They were each decorated all around with something that looked like a net made of bronze chains connecting bronze pomegranates.
Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
18 Nebuzaradan took with him to Babylon Seraiah the Supreme Priest, Zephaniah his assistant, and the three men who guarded the entrance [to the temple].
Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
19 And they found people who were still hiding in Jerusalem. From those people he took one officer from the Judean army, five of the king’s advisors, the chief secretary of the army commander who was in charge of recruiting men to join the army, and 60 other important Judean men.
Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
20 Nebuzaradan took them all to the king of Babylon at Riblah [city].
Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
21 There at Riblah, in Hamath province, the king of Babylon commanded that they all be executed. That is what happened when the people of Judah were (taken forcefully/exiled) from their land [to Babylon].
A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
22 Then King Nebuchadnezzar appointed Gedaliah, who was the son of Ahikam and grandson of Shaphan, to be the governor of the people who were still living in Judah.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
23 When all the army captains of Judah and their soldiers who had not surrendered to Nebuchadnezzar found out that the king of Babylon had appointed Gedaliah to be the governor, they met with him at Mizpah [town]. These army captains were Ishmael the son of Nethaniah, Johanan the son of Kareah, Seraiah the son of Tanhumeth from Netophah [town], and Jaazaniah from the Maacah region.
Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
24 Gedaliah solemnly promised them [that the officials from Babylon were not planning to harm them]. He said, “You may live in this land [without being afraid] and serve the king of Babylon, and [if you do], everything will go well for you.”
Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
25 But in October of that year, Ishmael, whose grandfather Elishama was one of the relatives of the descendants of King David, went to Mizpah along with ten other men and assassinated/killed Gedaliah and all the men who were with him. There were also men from Judah and men from Babylon whom they assassinated.
Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
26 Then many [HYP] of the people from Judah, important people and unimportant ones, and the army captains, were very afraid of [what] the Babylonians [would do to them], so they fled to Egypt.
Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
27 Thirty-seven years after King Jehoiachin of Judah was taken to Babylon, [Nebuchadnezzar’s son] Evil-Merodach became the king of Babylon. He was kind to Jehoiachin, and on April 2 of that year, he released/freed Jehoiachin from prison.
A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
28 He always spoke kindly to Jehoiachin and honored him more than the other kings who had been taken/exiled to Babylon.
Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
29 He gave Jehoiachin new clothes to replace the clothes that he had been wearing in prison, and he allowed Jehoiachin to eat at the king’s table every day for the rest of his life.
Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
30 The king of Babylon also gave him money every day, so that he could buy the things that he needed. The king continued to do that until Jehoiachin died.
Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.