< 2 Kings 24 >

1 While Jehoiakim was ruling [Judah, the army of] King Nebuchadnezzar of Babylon invaded Judah. [They defeated the Judean army, and as a result, ] Jehoiakim was required to pay a lot of tribute/taxes to King Nebuchadnezzar. But after three years, Jehoiakim rebelled.
A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
2 Then Yahweh sent raiders from Babylonia and Syria, and from the Moab and Ammon people-groups, to attack the people of Judah and get rid of them, just as Yahweh had told his prophets to warn the people would happen.
Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
3 These things happened to the people of Judah according to what Yahweh commanded. [He had decided] to get rid of the people of Judah because of the many sins that King Manasseh [had committed].
Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
4 Manasseh had even caused many innocent people in Jerusalem to be killed, and Yahweh would not forgive that.
haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
5 The other things that happened while Jehoiakim was king, and all the things that he did, are written in the scroll called ‘The History of the Kings of Judah’.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
6 When Jehoiakim died, his son Jehoiachin became the king.
Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
7 [The army of] the king of Babylon [defeated the army of Egypt, and] took control of all the area that the Egyptians formerly controlled, from the brook [at the border] of Egypt [in the south] to the Euphrates River [in the north]. So [the army of] the king of Egypt did not return [to attack Judah] again.
Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
8 Jehoiachin was 18 years old when he became the king of Judah. His mother’s name was Nehushta; she was the daughter of a man from Jerusalem named Elnathan. Jehoiachin ruled in Jerusalem for [only] three months.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
9 Jehoiachin did many things that Yahweh considered to be evil, just as his father had done.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
10 [While Jehoiachin was king, ] some officers of King Nebuchadnezzar of Babylon came [along with the whole Babylonian army] to Jerusalem, and they surrounded the city.
A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
11 While they were doing that, Nebuchadnezzar himself came to the city.
Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
12 Then King Jehoiachin and his mother and his advisors and important officers and palace officials all surrendered to the Babylonian army. These thngs happened when Nebuchadnezzar had been king for eight years. He arrested Jehoiachin and took him to Babylon.
Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
13 Just as Yahweh had said would happen, Nebuchadnezzar’s [soldiers] took [to Babylon] all the valuable things from Yahweh’s temple and from the king’s palace. They cut apart all the gold items that King Solomon had put in the temple.
Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
14 They took from Jerusalem [to Babylon] 10,000 people, including the important officials and the best soldiers and the people who made and repaired things that were made of metal. Only the very poor people were left in Judah.
Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
15 Nebuchadnezzar’s soldiers also took to Babylon Jehoiachin’s wives and officials, his mother, and [all] the important people.
Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
16 They also took to Babylon 7,000 of the best soldiers and 1,000 men who knew how to make and repair things that are made from metal. All of these people whom they took were strong and able to fight in wars.
Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
17 Then the king of Babylon appointed Jehoiachin’s uncle, Mattaniah, to be the king [of Judah], and he changed Mattaniah’s name to Zedekiah.
Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
18 When Zedekiah was twenty-one years old, he became king, and he ruled in Jerusalem for eleven years. His mother’s name was Hamutal; she was the daughter of a man named Jeremiah from Libnah [town].
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
19 But Zedekiah did many things that Yahweh considered to be evil, just as Jehoiakim had done.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
20 Yahweh was very angry. So (and finally/after he had been patient a long time) he expelled the people of Jerusalem and [the other places in] Judah and sent them to Babylon. [That is what happened when] Zedekiah rebelled against the king of Babylon.
Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.

< 2 Kings 24 >