< 2 Kings 13 >

1 After Joash had been ruling Judah for almost 23 years, Jehu’s son Jehoahaz became the king of Israel. He ruled in Samaria [city] for 17 years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 He did many things that Yahweh considered to be evil and committed the same kind of sins that Jeroboam had committed, sins which led the people of Israel to sin. He did not stop committing those sins.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 So Yahweh became very angry with the Israeli people, and he allowed the army of King Hazael of Syria and his son Ben-Hadad to defeat the Israelis many times.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Then Jehoahaz prayed to Yahweh [for help], and Yahweh heeded him, because he saw that the army of the king of Syria was oppressing the Israelis.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 Yahweh sent a leader to Israel, who enabled them to be freed from being controlled by Syria. After that, the Israeli people lived peacefully as they had done previously.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 But they still continued to commit the same kind of sins that Jeroboam and his family had committed and which led the Israelis to [also] sin. And the statue of the goddess Asherah remained in Samaria.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 Jehoahaz had only 50 men who rode on horses and ten chariots and 10,000 other soldiers, because the army of Syria had killed all the rest, trampling them like people walk on dirt.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 [If you want to read about] [RHQ] everything else that Jehoahaz did, you can read about it in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 Jehoahaz died [EUP] and was buried in Samaria. Then his son Jehoash became the king.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 Jehoash, the son of Jehoahaz, started to rule in Israel after King Joash had been ruling in Judah for 23 years. Jehoash ruled in Samaria for 17 years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 He did many things that Yahweh considered to be evil. He refused to turn away from worshiping idols, which was the sin that [many years earlier King] Jeroboam had told the Israeli people to commit.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 The other things that happened while Jehoash was king and all the things that he did are written in the book called ‘The Account of What the Kings of Israel Did’. In that account they wrote about Jehoash’s [army’s] victories, and their war with [the army of] King Amaziah of Judah.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 When Jehoash died, he was buried in Samaria where the [other] kings of Israel were buried. Then his son Jeroboam became king.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Elisha became very ill. Just before he died, King Jehoash went to Elisha and cried in front of him. [Saying the same words that Elisha had said when Elijah was taken to heaven], he said, “My father/master! My father/master! The chariots of us Israeli people and their drivers [are taking my master away]!”
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Elisha said to him, “Bring to me a bow and some arrows!” So the king did that.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Then Elisha told the king to put his hands on the bow [and prepare to shoot some arrows]. And then Elisha put his own hands on the king’s hands.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 Then Elisha told him, “[Have someone] open that window toward the east.” So they opened it. Then Elisha said, “Shoot!” So the king did. Then Elisha said, “That is the arrow that [indicates that your army] will defeat the Syrian army. Your army will completely defeat their [army] at Aphek [town].”
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Then Elisha said, “Pick up the other arrows and strike the ground with them!” So the king picked up the arrows and struck the ground three times.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 But Elisha was angry with him. He exclaimed, “You should have struck the ground five or six times! If you had done that, your army would have defeated the Syrian [army] until they were completely wiped out! But now, [because you struck the ground only three times, ] your army will defeat them only three times!”
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Then Elisha died and was buried. Groups of raiders from Moab came to Israel each year during (spring/the time when the cold season was ending).
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 One year, when some Israeli people were burying a man’s body, they saw a group of those raiders. [They were afraid, ] so quickly they threw that man’s body into the tomb where Elisha [had been buried, and they ran away]. But as soon as the man’s body touched Elisha’s bones, the dead man became alive again and jumped up!
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 King Hazael of Syria [sent soldiers to] oppress the Israeli people all during the years that Jehoahaz [ruled Judah].
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 But Yahweh was very kind [DOU] to the Israeli people. He helped them because of the agreement that he had made with [their ancestors] Abraham, Isaac, and Jacob. He did not get rid of the Israelis, and he still has not rejected them.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 When Hazael the king of Syria died, his son Ben-Hadad became the king.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 [The army of] King Jehoash of Israel defeated [the army of] King Ben-Hadad three times, and recaptured the cities that Ben-Hadad’s army had captured during the time that Jehoash’s father Jehoahaz was ruling Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >