< 2 Chronicles 7 >

1 When Solomon finished praying, fire came down from the sky and burned all the offerings and sacrifices [that were on the altar], and the glorious radiance of Yahweh filled the temple.
Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
2 The radiance [was extremely bright], with the result that the priests could not enter the temple of Yahweh.
Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
3 When all the Israeli people [who were there] saw the fire coming down and the glory of Yahweh above the temple, they prostrated themselves with their faces touching the ground. They worshiped and thanked Yahweh, singing, “Yahweh is always good to us; he faithfully loves us forever.”
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
4 Then the king and all the people who were there dedicated the temple to Yahweh by offering more sacrifices to him. King Solomon gave 22,000 cattle and 120,000 sheep and goats to be sacrificed.
Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
5
Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
6 The priests stood in their positions, and the other descendants of Levi stood in their positions holding the musical instruments [to praise] Yahweh, instruments that King David had caused to be made for praising Yahweh and thanking him. [They sang], “He faithfully loves us forever.” Facing the other descendants of Levi the priests stood, blowing their trumpets, while all the Israeli people were standing [and listening].
Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
7 Solomon dedicated the middle part of the courtyard in front of the temple. Then he gave offerings to be completely burned there along with the fat of the animals to be sacrificed to maintain fellowship with Yahweh. The priests burned them there in the courtyard because in addition to those things there were offerings of grain, with the result that there was not enough space on the bronze altar to burn all those sacrifices.
Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
8 Solomon [and the other people] celebrated the Festival of Living in Temporary Shelters for seven days. There was a huge group of people who celebrated with him. Some of them came from [as far away as] Lebo-Hamath [in the far north] and the border of Egypt [in the far south].
Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
9 On the eighth/next day they gathered again [to worship Yahweh]. They had celebrated the dedication of the altar for seven days and the Festival of Living in Temporary Shelters for seven days.
A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
10 Then on the next day Solomon sent them to their homes. They were very joyful because of all the good things that Yahweh had done for David and Solomon and for all his Israeli people.
A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
11 Solomon’s [workers] finished building the temple and Solomon’s palace. And Solomon finished doing everything else that he had planned to do.
Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
12 Then Yahweh appeared to him one night [in a dream] and said to him, “I have heard your prayer, and I have chosen this temple to be the place where my people will offer sacrifices to me.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
13 “When I prevent any rain from falling, or when I command locusts to eat all the crops, or when I send a plague among my people,
“Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
14 if the people who belong to me humble themselves and pray, and request me to help them, and if they turn away from their sinful behavior, then I will hear from heaven. I will forgive them for having sinned and I will cause them to prosper again.
in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
15 I [SYN] will see them and I [SYN] will hear them when they pray to me in this place.
Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
16 I have chosen and have (set apart/dedicated) this temple in order that people may worship [MTY] me there forever. I will always watch over [MTY] it and protect [IDM] it.
Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
17 “And as for you, if you obey me as David your father did, and if you do all that I command you to do, and obey all my laws and decrees,
“Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
18 I will make sure that your descendants will always be kings, which is what I promised to David your father, saying, ‘Some of your descendants will always be the kings of Israel.’
zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
19 “But if you Israelis turn away from me and disobey the decrees and commands that I have given to you, and you start to worship other gods,
“Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
20 I will cause you to be expelled from this land that I have given to you, and I will abandon this temple that I have set apart to be the place where people should worship me. I will cause it to be despised and ridiculed by people of all nations.
zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
21 Although this temple is now greatly respected, when that happens, all the people who pass by will be appalled, and they will say, ‘Why has Yahweh done terrible things like this to this country and to this temple?’
Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
22 And others will reply, ‘It happened because they rejected Yahweh, the God to whom their ancestors belonged, the one who brought their ancestors out of Egypt, and they have been worshiping other gods and trying to please them. And that is why Yahweh has caused them to experience all these disasters.’”
Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”

< 2 Chronicles 7 >