< 2 Chronicles 33 >

1 Manasseh was 12 years old when he became the king [of Judah], and he ruled from Jerusalem for 55 years.
Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
2 He did many things that Yahweh considered to be evil. He imitated the disgusting things that were formerly done by the people-groups that Yahweh had expelled from Israel as his people advanced [though the land].
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 He commanded his workers to rebuild the shrines [for worshiping idols] that his father Hezekiah had destroyed. He told them to set up altars to [honor] the statues of Baal, and to make altars to [honor the goddess] Asherah. He bowed down to [worship] all the stars.
Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
4 He directed his workers to build altars [for foreign gods] in the temple, about which Yahweh had said, “It is here in Jerusalem that I want people to worship me, forever.”
Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
5 He directed that altars for [worshiping] all the stars be built in both of the courtyards outside the temple.
Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
6 He even sacrificed [some of] his own sons and burned them in a fire in Hinnom Valley. He performed rituals to practice sorcery. He asked fortune-tellers for advice. He performed witchcraft. He talked to people who consulted the spirits of people who had died to find out what would happen in the future. He did many things that Yahweh considered o be very evil, things that caused Yahweh to become very angry.
Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
7 Manasseh took a carved idol [that his workers had made] and put it in the temple. That is the temple concerning which God had said to David and to his son Solomon, “My temple will be here in Jerusalem, the city that I have chosen [where I want people to] worship me, forever.
Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 If they will obey all the laws and decrees and regulations that I told Moses to give to them, I will not again force the Israeli people to leave this land that I gave to their ancestors.”
Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
9 But Manasseh led the people of Jerusalem and other places in Judah to do things that are wrong, with the result that they did more evil than was done by the people in the people-groups that Yahweh had expelled as the Israeli people advanced [through the land].
Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Yahweh spoke to Manasseh and the people of Judah, but they paid no attention.
Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
11 So Yahweh caused the army commanders of Assyria [and their soldiers] to [come to Jerusalem, and they] captured Manasseh. They put a hook in his nose and put bronze chains on his [feet] and took him to Babylon.
Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
12 There, while he was suffering, he humbled himself greatly in the presence of Yahweh, the God whom his ancestors [worshiped], and pleaded with Yahweh to help him.
Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
13 When he prayed, Yahweh heard him and pitied him. So he [allowed him to] return to Jerusalem and [to] rule his kingdom again. Then Manasseh realized that Yahweh is [an all-powerful] God.
Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
14 Later, Manasseh’s [workers] rebuilt the eastern section of the outer wall around Jerusalem, and [they] made it higher. That section extended from Gihon Spring [north] to the Fish Gate, and around the part of the city that they called Ophel [Hill]. Manasseh also appointed army officers to guard each of the cities in Judah that had walls around them.
Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
15 Manasseh’s [workers] removed from the temple the idols and the stone statues of gods of other nations. Manasseh also [told them to] remove the altars that they had previously built on Zion Hill and in [other places in] Jerusalem. He had all those things thrown out of the city.
Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
16 Then he [told them to] repair the altar of Yahweh, and he offered sacrifices to restore fellowship with Yahweh and to thank him. And he told [the people of] Judah that they must worship [only] Yahweh.
Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
17 The people continued to offer sacrifices on the hilltops, but only to Yahweh their God.
Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
18 The other things that happened while Manasseh was ruling, including his prayer to God and the messages from Yahweh that the prophets gave to him, are written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
19 What Manasseh prayed and how God pitied him because he pleaded to God, and also his sins and ways in which he disobeyed God, and the [list of] places where he built shrines and set up poles to [honor the goddess] Asherah and other idols [before he humbled himself], are written in what the prophets wrote.
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
20 Manasseh died and was buried in his palace. Then his son Amon became the king [of Judah].
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Amon was 22 years old when he became king, and he ruled in Jerusalem for two years.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
22 He did things that Yahweh considered to be evil, like his father Manasseh had done. Amon worshiped all the idols that Manasseh’s [workers] had made.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
23 But he did not humble himself and turn to Yahweh like his father did. So he became more sinful than his father had been.
Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
24 Then Amon’s officials made plans to kill him. They assassinated him in his palace.
Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
25 But then the people of Judah killed all those who had assassinated Amon, and they appointed his son Josiah to be their king.
Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.

< 2 Chronicles 33 >