< 2 Chronicles 23 >

1 After Joash had been hidden in the temple for six years, Jehoiada the priest decided that it was necessary to do something. So he made an agreement with the army commanders of groups of 100 soldiers: Azariah the son of Jeroham, Ishmael the son of Jehohanan, Azariah the son of Obed, Maaseiah the son of Adaiah, and Elishaphat the son of Zicri.
A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
2 They went throughout Judah and gathered the descendants of Levi and the leaders of Israeli families from all the towns. When they came to Jerusalem,
Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
3 the whole group went to the temple and made an agreement with the young king there. Jehoiada said to them, “This is the son of the previous king of Judah. So he is the one who must rule, like Yahweh promised that the descendants of King David must do.
dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
4 “So this is what you must do: One-third of you priests and other descendants of Levi who are starting their work on the Sabbath day must guard the doors [of the temple].
Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
5 One-third of you must guard the king’s palace, and one-third of you must guard the Foundation Gate. All the other people will be in the courtyards outside the temple.
kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
6 Only the priests and the descendants of Levi who work there will enter the temple. They will be allowed to enter the temple because they are set apart [for that work]. All the others must remain in the courtyards, obeying what Yahweh has commanded.
Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
7 You descendants of Levi must stand around the young king, each of you with your weapon in your hand. Anyone else who tries to enter the temple you must kill. And stay close to the young king, wherever he goes.”
Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
8 So the descendants of Levi and all [the men of] Judah did what Jehoiada had told them. He did not allow anyone to go home after having finished his work on that Sabbath day. Each commander took charge of his men, the ones who were finishing their work on that day and those who were starting their work on that day.
Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
9 Then Jehoiada gave each of the commanders the spears and the large and small shields that had been put there in the temple by King David.
Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
10 He commanded all the guards to stand in their positions, each with his sword in his hand, all around the king—around the altar and the temple, from the north side to the south side.
Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
11 Then Jehoiada and his sons brought Joash out. They put a crown on his head and gave him [a scroll] on which were written the rules [that the kings needed to obey], and proclaimed that he was now the king. They anointed him with olive oil and shouted, “We hope that the king will live for many years!”
Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
12 When Athaliah heard the noise being made by the people running [toward the king] and cheering, she ran to the temple.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
13 She saw the young king there, standing alongside the pillar at the entrance of the temple, [which is the place at the temple] where the kings usually stood. The army commanders and trumpet players were standing beside the king, and all the people of Judah were rejoicing and blowing trumpets, and singers with their musical instruments were leading the people while they praised God. Then Athaliah tore her robes and started screaming, “You are committing treason!”
Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
14 Jehoiada the Supreme Priest said to the army commanders, “Kill her, but do not kill her at the temple of Yahweh!” Then he said to them, “Bring Athaliah out in front of the troops and kill anyone who tries to follow her!”
Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
15 [She tried to flee, but] they seized her as she reached the gate where horses enter the palace area, and they killed her there.
Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
16 Then Jehoiada made an agreement that he and the king and all the other people would be Yahweh’s people.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
17 Then all the people who were there went to the temple of Baal and tore it down. They smashed the altars [of Baal]. They also killed Mattan, the priest of Baal, in front of those altars.
Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
18 Then Jehoiada appointed the priests, who were also descended from Levi, to work at the temple. They were part of the group to whom King David had given various jobs at the temple, to sacrifice the animals that were to be completely burned on the altar, doing what was written in the laws that Moses had given to them. He also told them to rejoice and sing, which was also what David had commanded.
Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
19 He also put guards at the gates of the temple in order that anyone who was unacceptable to God would not be allowed to enter.
Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
20 Jehoiada took with him the army commanders, the important men, the leaders and many others, and brought the king down from the temple. They went into the palace through the Upper Gate, and put the king on his throne.
Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
21 Then all the people of Judah rejoiced. And there was calm throughout the city, because Athaliah had been killed.
sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.

< 2 Chronicles 23 >