< 2 Chronicles 21 >

1 Then Jehoshaphat died, and was buried where his ancestors were buried in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’. Then his son Jehoram became the king [of Judah].
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 His [younger] brothers were Azariah, Jehiel, Zechariah, Azariah, Michael, and Shephatiah.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 Before Jehoshaphat died, he gave them gifts of silver and gold and other valuable things. He also appointed them to rule various cities in Judah that had walls around them. But he appointed Jehoram to be the king of Judah, because Jehoram was his oldest son.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 After Jehoram was completely in control of his father’s kingdom, he had all of his [younger] brothers executed, along with some of the leaders of the nation.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Jehoram was 32 years old when he became the king, and he ruled in Jerusalem for eight years.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 But he did many of the [evil] things that the kings of Israel had done. He did many things that Yahweh considers to be evil, things that the family of Ahab had done, because he married one of Ahab’s daughters.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 However, because of the agreement that Yahweh had made with King David, Yahweh did not want to get rid of the descendants of David. He had promised that David’s descendants would always be the ones who ruled Judah.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 While Jehoram was ruling, the people of [the] Edom [region] rebelled against [the king of] Judah and appointed their own king.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 So Jehoram and his officers and his men in chariots went to Edom. There, the army of Edom surrounded them. Jehoram escaped during the night.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 But the king of Judah was never able to regain control of Edom, and Edom is still not controlled by Judah. [The people in] Libnah [city between Judah and Philistia] also rebelled against Judah. Those things happened because Jehoram turned away from [obeying] Yahweh, the God whom his ancestors [belonged to].
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 On the hilltops in Judah he had also built shrines [to worship idols], and had caused the people of Judah to stray away from Yahweh by worshiping foreign gods.
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 One day, Jehoram received a letter from the prophet Elijah. Elijah had written this in the letter: “This is what Yahweh, the God whom your ancestor [King] David [worshiped], says: 'You have not done things that please me like your father Jehoshaphat did or what King Asa did.
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 Instead, you have continually done the [evil things] that the kings of Israel have done. You have encouraged the people in Jerusalem and other places in Judah to stop worshiping Yahweh, like the descendants of Ahab did. You have also murdered your own brothers, who were more righteous men than you are.
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 So now Yahweh is about to very severely punish the people in your kingdom and even your own children and your wives and everything that you own.
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 And you yourself will have an intestinal disease that will continue to become worse, and you will suffer from it until you die.'”
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 Then Yahweh caused some men from the Philistia people-group and some Arabs who lived near the coast [of the Mediterranean Sea], where people from Ethiopia had settled, to become angry with Jehoram.
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 Their army invaded Judah and took away [from Jerusalem] all the valuable things that they found in the king’s palace, and even his sons and wives. His youngest son, Ahaziah, was the only one of his sons whom they did not take away.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 After that happened, Yahweh caused Jehoram to be afflicted with an intestinal disease that no one could cure.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 About two years later, while he was in great pain, he died because of that disease. The people of Judah had made bonfires to honor his ancestors when they died, but they did not make a bonfire for Jehoram.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 Jehoram was 32 years old when he became the king, and he ruled in Jerusalem for eight years. No one was sorry when he died. His corpse was buried in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’, but he was not buried where the other kings [of Judah] had been buried.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

< 2 Chronicles 21 >