< 2 Chronicles 19 >

1 When King Jehoshaphat was returning safely to his palace in Jerusalem,
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 the prophet Jehu, the son of [the prophet] Hanani, went out of the city to meet the king, and said to him, “It was not right for you to help a wicked man and to love those who hate Yahweh. Because of what you have done, Yahweh is angry with you.
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 But you have done some good things; you got rid of the poles in this country for [worshiping the goddess] Asherah, and you have strongly determined to do what pleases God.”
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 Jehoshaphat lived in Jerusalem. But [one time], like he had done once previously, he went out among all the people in the country, from Beersheba [city in the far south] to the hilly area of [the tribe of] Ephraim [in the far north], and he convinced them to return to [worshiping] Yahweh, the God whom their ancestors [worshiped].
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 He appointed judges throughout Judah, in each of the cities that had walls around them.
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 He told them, “Make your decisions carefully, because you are judging cases not [in order] to [please] people but to [please] Yahweh. And he will be watching you whenever you make a decision.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 So now revere Yahweh, and judge cases carefully, [and do not forget that] Yahweh our God never acts unjustly, and he never does what people want because of their offering him money; he never accepts bribes.”
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 In Jerusalem also, Jehoshaphat appointed some priests and other descendants of Levi and some leaders of Israeli families [to be judges]. He told them to do what Yahweh’s laws said was right when they settled disputes. Those men lived in Jerusalem.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 He told them this: “You must always do your work faithfully, revering Yahweh.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 In every dispute that your fellow Israelis who live in the cities want you to settle, you must warn them to not sin against Yahweh [by telling lies during the trial]. If you do not warn them, God will punish both you and your fellow Israelis. If you warn them, you will not be sinning. You must warn them whether [someone has accused them] of murdering someone, or of disobeying some other law or command or decree [of Yahweh].
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 Amariah the Supreme Priest will supervise you in any matter that Yahweh is concerned about, and Zebadiah the son of Ishmael, the leader of the tribe of Judah, will supervise you in any matter that I am responsible for. And the descendants of Levi will assist you. Act courageously, and I pray that Yahweh will help those who do their work well.”
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”

< 2 Chronicles 19 >