< 2 Chronicles 15 >
1 The Spirit of God came upon Azariah, the son of Obed.
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
2 Azariah went to talk with Asa, and said to him, “Asa and all [you men of the tribes of] Judah and Benjamin, listen to me. Yahweh is with you whenever you are trusting in him. If you request him [to help you], he will help you, but if you abandon him, he will abandon you.
Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
3 For many years the Israeli people did not know the true God, and they did not have priests or God’s laws.
Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
4 But when they experienced trouble, they turned to Yahweh our God, and requested him to help them. And he helped them.
Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
5 At that time, people were not safe when they traveled, because all the people who lived in the nearby countries were experiencing many difficulties.
A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
6 The people of various nations were thoroughly defeated by [armies of] other nations, and people in some cities were crushed by [armies from] other cities, because God was allowing them to experience many difficulties.
Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
7 But you people, you must be strong and do not become discouraged, because [God] will reward you for what you do [to please him.”]
Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
8 When Asa heard what the prophet Azariah said, he was encouraged. He [commanded his workers to] remove all the detestable idols from everywhere in the land of the tribes of Judah and Benjamin, and from the towns that [his soldiers] had captured in the hills of the tribe of Ephraim. Asa’s workers repaired the altar [where people offered sacrifices] to Yahweh that was in front of the entrance to the temple [in Jerusalem].
Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
9 Then he gathered all [the people of the tribes of] Judah and Benjamin and many people from the tribes of Ephraim, Manasseh, and Simeon who were living among them. [He was able to do that] because many people from [those tribes in] Israel had come to me to Judah when they realized that Yahweh, the God that Asa [worshiped], was helping him.
Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
10 After Asa had been ruling for almost 15 years, in May of that year, those people gathered in Jerusalem.
Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
11 At that time they sacrificed to Yahweh 700 bulls and 7,000 sheep and goats, from the animals that they had captured [when they defeated the army of Ethiopia/Sudan].
A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
12 They solemnly made an agreement to very sincerely worship Yahweh, the God whom their ancestors [worshiped].
Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
13 They promised to execute all those who would not worship Yahweh, including those who were important and those who were not important, both men and women.
Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
14 They shouted and blew trumpets and other horns while they solemnly promised to do that.
Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
15 All the people who were living in Judah were happy with the agreement because they had solemnly and very sincerely promised to keep it. They eagerly requested help from Yahweh, and he helped them. So he enabled them to have peace throughout their country.
Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
16 King Asa’s grandmother Maacah had made a disgusting pole for [worshiping the goddess] Asherah. So Asa [commanded his workers to] cut down that pole and chop it into pieces and burn it in the Kidron Valley. He then did not allow Maacah to continue [to influence the people because of her] being the mother of the previous king.
Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
17 Although Asa’s [workers] did not get rid of the shrines on the hilltops in Israel, he was very determined to [do what] pleased Yahweh all his life.
Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
18 He [ordered his workers to] bring into God’s temple all the silver and gold and other valuable items that he and his father had dedicated [to God].
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
19 There were no more wars [in Judah] until Asa had been ruling Judah almost 35 years.
Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.